< 2 Crónicas 7 >

1 Ahora, cuando las oraciones de Salomón terminaron, el fuego bajó del cielo, quemando todas las ofrendas; y el templo se llenó de la gloria de él Señor.
Sa’ad da Solomon ya gama yin addu’a, sai wuta ya sauko daga sama ya cinye hadaya ta ƙonawa da kuma sadakokin, ɗaukakar Ubangiji kuwa ta cika haikalin.
2 Y los sacerdotes no pudieron entrar en el templo del Señor, porque la casa del Señor estaba llena de la gloria del Señor.
Firistoci ba su iya shiga haikalin Ubangiji ba domin ɗaukakar Ubangiji ta cika shi.
3 Y todos los hijos de Israel estaban mirando cuando el fuego bajó, y la gloria del Señor estaba en la casa; y se arrodillaron, con sus caras hacia la tierra, adorando y alabando al Señor, y diciendo: Él es bueno; porque su misericordia es para siempre.
Sa’ad da dukan Isra’ilawa suka ga wutar na saukowa, ɗaukakar Ubangiji kuma tana a bisa haikalin, sai suka durƙusa a dakali da fuskokinsu a ƙasa, suka yi sujada suka kuma yi godiya ga Ubangiji suna cewa, “Ubangiji mai alheri ne, ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.”
4 Entonces el rey y todo el pueblo hicieron ofrendas delante del Señor.
Sai sarki da dukan mutanen suka miƙa hadayu a gaban Ubangiji.
5 El rey Salomón hizo una ofrenda de veintidós mil bueyes y ciento veinte mil ovejas. Así que el rey y todo el pueblo celebraron la fiesta de la dedicación del templo de Dios.
Sarki Solomon kuwa ya miƙa hadayar bijimai dubu ashirin da biyu da kuma tumaki da awaki dubu ɗari da dubu ashirin. Ta haka sarki da dukan mutane suka keɓe haikalin Allah.
6 Y los sacerdotes estaban en sus lugares, y los levitas con sus instrumentos musicales para el canto del Señor, que David el rey había hecho para la alabanza del Señor, cuya misericordia es para siempre, cuando David cantaba con ellos y los sacerdotes sonaron cuernos delante de ellos; y todo Israel estaba de pie.
Firistoci suka ɗauki matsayinsu, haka kuma Lawiyawa suka tsaya a matsayinsu riƙe da kayansu na bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe na Ubangiji, waɗanda Sarki Dawuda ya yi domin yabon Ubangiji. An yi amfani da su sa’ad da ake godiya, ana kuma cewa, “Ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.” Kurkusa da Lawiyawa, firistoci suka busa ƙahoninsu, dukan Isra’ila kuwa suna a tsaye.
7 Entonces Salomón santificó la mitad del atrio frente al templo del Señor, ofreciendo allí las ofrendas quemadas y la grasa de las ofrendas de paz; porque no había lugar en el altar de bronce que Salomón había hecho para todas las ofrendas quemadas y las ofrendas de cereales y la grasa.
Solomon ya tsarkake sashen tsakiya na filin da yake gaban haikalin Ubangiji, a can ya miƙa hadayun ƙonawa da kitsen hadayun salama domin bagaden tagullar da ya yi ba zai iya ɗaukan hadayun ƙonawa, hadayun hatsi da kuma ɓangarori na kitsen ba.
8 Así que Salomón celebró la fiesta en ese tiempo durante siete días, y todo Israel con él, una reunión muy grande, porque la gente se había reunido desde Hamat y hasta el río de Egipto.
Ta haka Solomon ya kiyaye bikin a wannan lokaci har kwana bakwai, dukan Isra’ila kuwa tare da shi, babban taro, mutane daga Lebo Hamat har zuwa Rafin Masar.
9 Y al octavo día tuvieron una reunión santa; Las ofrendas para santificar el altar duraron siete días, y la fiesta solemne duró siete días.
A rana ta takwas sai suka yi taro, gama sun yi bikin keɓewar bagade na kwana bakwai da kuma biki na ƙarin kwana bakwai.
10 Y a los veintitrés días del mes séptimo, envió a la gente a sus tiendas, llenos de gozo y alegría en sus corazones, por todo el bien que el Señor había hecho a David a Salomón y a Israel su pueblo.
A rana ta ashirin da uku na watan bakwai sai ya sallami mutane su tafi gidajensu da farin ciki da kuma murna a zuciya saboda abubuwa masu kyau da Ubangiji ya yi domin Dawuda da Solomon da kuma domin mutanensa Isra’ila.
11 Entonces Salomón llegó al final de la construcción del templo del Señor y del palacio del rey; y todo lo que estaba en su mente para hacer en él templo del Señor y para sí mismo había sido bien hecho.
Sa’ad da Solomon ya gama haikalin Ubangiji da kuma fadan sarki ya kuma yi nasara a yin dukan abin da yake a zuciyarsa da zai yi a haikalin Ubangiji da kuma a fadarsa,
12 Entonces el Señor vino a Salomón en una visión nocturna y le dijo: He escuchado tu oración, y he tomado este lugar para mí como una casa donde se deben hacer ofrendas.
sai Ubangiji ya bayyana gare shi a daren ya ce, “Na ji addu’arka na kuma zaɓi wannan wuri don kaina, a matsayin haikali don hadayu.
13 Si, en mi palabra, el cielo está cerrado, para que no llueva, o si envío langostas sobre la tierra para su destrucción, o si envío enfermedad a mi pueblo;
“Sa’ad da na kulle sammai don kada a yi ruwan sama ko na umarci fāri su cinye amfanin ƙasar ko kuwa na aika da annoba a cikin mutanena,
14 Si mi pueblo, de quien recibe mi nombre, se humilla y se acerca a mí en oración, buscándome y apartándose de sus malos caminos; entonces escucharé desde el cielo, ignorando su pecado, y sanaré su tierra.
in mutanena, waɗanda ake kira da sunana, sun ƙasƙantar da kansu, suka kuma yi addu’a, suka nemi fuskata, suka kuma juye daga mugayen hanyoyinsu, zan ji daga sama in kuma gafarta zunubinsu in kuwa warkar da ƙasarsu.
15 Ahora mis ojos estarán abiertos y mis oídos atentos a las oraciones hechas en este lugar.
Yanzu, idanuna za su buɗu, kunnuwata kuma za su saurara ga addu’o’in da aka miƙa a wannan wuri.
16 Porque he tomado esta casa para mí y la he santificado, para que mi nombre esté allí para siempre; y mis ojos y mi corazón estarán allí en todo momento.
Na zaɓi na kuma tsarkake wannan haikali saboda Sunana yă kasance a can har abada. Idanuna da kuma zuciyata kullum za su kasance a can.
17 Y en cuanto a ti, si sigues tu camino delante de mí como lo hizo David tu padre, haciendo lo que te he ordenado y guardando mis leyes y mis decisiones:
“Game da kai kuwa, in ka yi tafiya a gabana kamar yadda Dawuda mahaifinka ya yi, ka kuma yi dukan abin da na umarta, ka kiyaye ƙa’idodina da dokokina,
18 Entonces fortaleceré el trono de tu reino, según el pacto que le di a David, tu padre, diciendo: Nunca estarás sin un hombre que sea gobernante en Israel.
zan kafa kujerar sarautarka, yadda na alkawarta wa Dawuda mahaifinka sa’ad da na ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani mutumin da zai yi mulki a bisa Isra’ila ba.’
19 Pero si te apartas de mí, y no guardas mis órdenes y mis leyes que he puesto delante de ti, sino vas y sirves a otros dioses, dándoles adoración:
“Amma in ka juya daga gare ni ka yashe ƙa’idodi da umarnan da na ba ka, ka yi gaban kanka don ka bauta wa waɗansu alloli ka kuma yi musu sujada,
20 Entonces haré que esta gente sea desarraigada de la tierra que les he dado; y esta casa, que he santificado para mi nombre, la apartaré de mis ojos, y la convertiré en un ejemplo y una palabra de vergüenza entre todos los pueblos.
zan tumɓuke Isra’ila daga ƙasata, wadda na ba su, zan kuma ƙi wannan haikalin da na tsarkake domin Sunana. Zan mai da shi abin karin magana da abin ba’a cikin dukan mutane.
21 Y este templo se convertirá en un montón de muros rotos, y todos los que pasen serán vencidos con asombro, y dirán: ¿Por qué el Señor lo ha hecho así a esta tierra y a este templo?
Ko da yake wannan haikali yanzu mai girma ne, dukan wanda ya wuce zai kaɗa kai yă ce, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi irin wannan abu ga wannan ƙasa da kuma ga wannan haikali?’
22 Y su respuesta será: Porque fueron rechazados del Señor, el Dios de sus padres, que los sacaron de la tierra de Egipto, y tomaron para sí otros dioses y los adoraron y se convirtieron en sus sirvientes. por eso ha enviado todo este mal sobre ellos.
Mutane za su amsa, ‘Domin sun yashe Ubangiji Allah na kakanninsu, wanda ya fitar da su daga Masar, suka rungumi waɗansu alloli, suna musu sujada, suna bauta musu, shi ya sa ya kawo dukan wannan masifa a kansu.’”

< 2 Crónicas 7 >