< 2 Crónicas 31 >

1 Ahora que todo esto había terminado, todos los hombres de Israel que estaban presentes salieron a las ciudades de Judá, causando que los pilares de piedra se rompieran y los pilares de madera representaciones de Asera, derribando los lugares altos y los altares en todo Judá y Benjamín, así como en Efraín y Manasés, hasta que todos se fueron. Entonces todos los hijos de Israel volvieron a sus ciudades, cada uno a su propiedad.
Sa’ad da aka gama dukan wannan, sai Isra’ilawan da suke can suka fita zuwa garuruwan Yahuda, suka rurrushe keɓaɓɓun duwatsu suka kuma farfashe ginshiƙan Ashera. Suka rurrushe masujadan kan tudu da bagadai, ko’ina a Yahuda da Benyamin da kuma cikin Efraim da Manasse. Bayan sun rurrushe dukansu, sai Isra’ilawa suka koma garuruwansu, kowanne zuwa mahallinsa.
2 Entonces Ezequías puso en orden los turnos de los sacerdotes y levitas, cada uno en su división, en relación con su servicio, por las ofrendas quemadas y las ofrendas de paz, y por la ordenación de la adoración y por alabar a Dios; y sirvieran en las puertas de la casa del Señor.
Hezekiya kuma ya raba firistoci da Lawiyawa kashi-kashi, kowanne da hidimarsa, firistoci da Lawiyawa, don hadayu na ƙonawa da na salama, su yi hidima, su yi godiya, su kuma rera yabai a ƙofofin mazaunin Ubangiji.
3 Y le dio al rey parte de su propiedad privada por las ofrendas quemadas, es decir, por las ofrendas de la mañana y de la tarde, y las ofrendas para el sábado y las lunas nuevas y las fiestas regulares, como se registra en la ley del Señor.
Sarki ya ba da taimako daga mallakarsa domin hadayun ƙonawa, safe da yamma da kuma don hadayun ƙonawa a Asabbatai, Sabon Wata da kuma ƙayyadaddun bukukkuwa kamar yadda yake a rubuce a cikin Dokar Ubangiji.
4 Además, dio órdenes a la gente de Jerusalén para que les dieran a los sacerdotes y levitas la parte que les pertenecía por derecho, para que pudieran ser fuertes en el cumplimiento de la ley del Señor.
Ya umarci mutanen da suke zama a Urushalima su ba da rabon da yake na firistoci da Lawiyawa, don su ƙwallafa ransu ga Dokar Ubangiji.
5 Y cuando se hizo pública la orden, los hijos de Israel dieron de inmediato, en grandes cantidades, los primeros frutos de su grano y vino y aceite y miel, y del producto de sus campos; y tomaron en una décima parte de todo, una gran cantidad.
Nan da nan aka baza umarnin, sai Isra’ilawa suka bayar’ya’yan farin hatsinsu, sabon ruwan inabi, mai da kuma zuma da dukan abin da gona ta bayar, hannu sake. Suka kawo zakan kowane abu da yawa.
6 Y los hijos de Israel y Judá, que vivían en las ciudades de Judá, vinieron con la décima parte de sus bueyes y ovejas, y una décima parte de todas las cosas consagradas que debían ser dadas al Señor su Dios, y los pusieron por montones.
Mutanen Isra’ila da Yahuda waɗanda suke zama a garuruwan Yahuda, su ma suka kawo zakan shanu da na tumaki da kuma zakan abubuwa masu tsarki da aka keɓe ga Ubangiji Allahnsu, suka jibge su tsibi-tsibi.
7 La primera reserva de cosas se dejó en el tercer mes, y en el séptimo mes terminaron.
Sun fara yin haka a wata na uku, suka kuma gama a wata na bakwai.
8 Y cuando Ezequías y los gobernantes vinieron y vieron toda la reserva de bienes, alabaron al Señor y a su pueblo Israel.
Sa’ad da Hezekiya da fadawansa suka zo suka ga tsibin, sai suka yabi Ubangiji, suka kuma albarkace mutanensa Isra’ila.
9 Entonces Ezequías hizo preguntas a los sacerdotes y levitas sobre el almacén de bienes.
Hezekiya ya tambayi firistoci da Lawiyawa game da tsibin;
10 Y Azarías, el principal sacerdote de la familia de Sadoc, dijo en respuesta: Desde el momento en que las personas llegaron por primera vez con sus ofrendas a la casa del Señor, hemos comido lo suficiente, y más que suficiente, porque la bendición del Señor está sobre su pueblo; Y toda esta cantidad a sobrado.
sai Azariya babban firist, daga iyalin Zadok ya amsa, “Tun daga lokacin da mutane suka fara kawo taimakonsu ga haikalin Ubangiji, muna da isashe don abinci da kuma da yawa da za mu rage, domin Ubangiji ya albarkaci mutanensa, saboda haka abin da ya ragu a rumbu yana da yawa.”
11 Entonces Ezequías dijo que los almacenes debían estar listos en la casa del Señor; y esto fue hecho.
Hezekiya ya ba da umarni a shirya ɗakunan ajiya a haikalin Ubangiji, aka kuwa yi haka.
12 Y en ellos pusieron todas las ofrendas, las décimas y las porciones consagradas, sin guardar nada, y sobre ellos estaba Conanias el levita, y a Simei, su hermano, le siguió.
Sa’an nan cikin aminci suka kawo taimako, zakka da keɓaɓɓun kyautai. Konaniya, wani Balawe, shi ne ke lura da waɗannan abubuwa, kuma ɗan’uwansa Shimeyi shi ne na biye da shi.
13 Y Jehiel, Azazias, Nahat, Asael y Jerimot y Jozabad y Eliel e Ismaquias, Mahat y Benaía eran supervisores, bajo la dirección de Conanias y Simei su hermano, por orden de Ezequías el rey y Azarías, el gobernante de la casa de Dios.
Yehiyel, Azaziya, Nahat, Asahel, Yerimot, Yozabad, Eliyel, Ismakiya, Mahat da Benahiya su ne shugabanni, mataimakan Konaniya da Shimeyi ɗan’uwansa, waɗanda sarki Hezekiya da Azariya babban shugaban haikalin Allah suka naɗa.
14 Y Core, el hijo de Imna el levita, el guardián de la puerta del este, tenía el control de las ofrendas dadas gratuitamente a Dios, y la distribución de las ofrendas del Señor y las porciones consagradas.
Kore ɗan Imna Balawe, mai tsaron Ƙofar Gabas, shi ne yake lura da baikon yardan ran da aka yi wa Allah, don ya karkasa bayarwar da aka keɓe domin Ubangiji da hadayu mafi tsarki.
15 Y debajo de él estaban Edén y Miniamin y Jesua y Semaías, Amarías y Secanias, en los pueblos de los sacerdotes, quienes se hicieron responsables de dar el reparto de las porciones, por turnos, a pequeños y grandes:
Eden, Miniyamin, Yeshuwa, Shemahiya, Amariya da Shekaniya sun taimake shi da aminci a cikin garuruwan firistoci, suna ba da rabo wa’yan’uwansu firistoci bisa ga sassansu, tsofaffi da yara.
16 Así como a todos los varones, de tres años y más, enumerados por sus familias, que entraron en la casa del Señor para hacer lo que se necesitaba día a día, para su trabajo especial con sus turnos.
Bugu da ƙari, suka ba da rabo ga maza’yan shekaru uku ko fiye waɗanda sunayensu suna a tarihin zuriya, dukan waɗanda ba za su iya shiga haikalin Ubangiji su yi ayyukansu na kullum ba, bisa ga nawayarsu da kuma sassansu.
17 Las familias de los sacerdotes fueron nombradas por los nombres de sus padres, pero los levitas, de veinte años en adelante, fueron listados en relación a su servicio en sus turnos;
Suka kuma ba da rabo ga firistocin da aka rubuta ta iyalansu cikin tarihin zuriya, haka kuma ga Lawiyawa masu shekara ashirin ko fiye, bisa ga nawayarsu da kuma sassansu.
18 Y en las listas estaban todos sus pequeños y sus esposas y sus hijos e hijas, todo la familia, porque se consagraban fielmente a la santidad.
Suka haɗa da dukan ƙanana’ya’yansu, mata, da kuma’ya’ya maza da’ya’ya mata, al’umma gaba ɗaya da aka jera a waɗannan tarihin zuriya. Gama sun yi aminci cikin tsarkake kansu.
19 Y en cuanto a los hijos de Aarón, los sacerdotes, que viven en el campo en las afueras de sus pueblos, en cada pueblo diferente había hombres, inscritos por su nombre, para dar su parte de los bienes a todos los hombres, entre los sacerdotes, y a todos los que estaban incluidos entre los levitas.
Akwai mutane a garuruwa da yawa waɗanda aka sa don su rarraba wa’ya’yan Haruna, firist, maza, waɗanda suke zaune a gonaki na ƙasar garuruwansu su ba kowane namijin da aka rubuta na Lawiyawa, rabonsa.
20 Esto hizo Ezequías a través de todo Judá; hizo lo que era bueno, correcto y verdadero delante del Señor su Dios.
Abin da Hezekiya ya yi ke nan ko’ina a Yahuda, yana yin abin da yake da kyau, daidai da kuma mai aminci a gaban Ubangiji Allahnsa.
21 Y por todo lo que hizo, en relación con el servicio del templo de Dios y su ley y sus órdenes, recibió instrucciones de Dios y lo hizo con un propósito serio; Y por eso fue prosperado.
Cikin kome da ya yi cikin hidimar haikalin Allah, cikin biyayya kuma ga doka da umarnai, ya nemi Allahnsa, ya kuma yi aiki gabagadi. Ta haka kuwa ya yi nasara.

< 2 Crónicas 31 >