< 2 Crónicas 24 >
1 Joás tenía siete años cuando comenzó a reinar, y gobernó durante cuarenta años en Jerusalén. Él nombre de su madre era Sibia de Beerseba.
Yowash yana da shekara goma sha bakwai sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi sarauta a Urushalima shekara arba’in. Sunan mahaifiyarsa Zibiya ce; ita daga Beyersheba.
2 Y Joás hizo lo que era correcto a los ojos del Señor mientras viviera Joiada, el sacerdote.
Yowash ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji duka shekarun Yehohiyada firist.
3 Y Joiada tomó dos esposas por él, y él fue padre de hijos e hijas.
Yehohiyada ya zaɓi mata biyu dominsa, yana kuma da’ya’ya maza da’ya’ya mata.
4 Después de esto, Joás tuvo el deseo de poner la casa del Señor en orden nuevamente;
Wani lokaci daga baya Yowash ya yanke shawara yă gyara haikalin Ubangiji.
5 Y reuniendo a los sacerdotes y levitas, les dijo: Salgan de las ciudades de Judá año tras año, y obtengan de todo el dinero de Israel para mantener la casa de su Dios en buenas condiciones; y ver que esto se hace sin pérdida de tiempo. Los levitas, sin embargo, tardaron en hacerlo.
Ya tara firistoci da Lawiyawa wuri ɗaya ya ce musu, “Ku je garuruwan Yahuda ku karɓa kuɗin da ya kamata a biya shekara-shekara daga dukan Isra’ila, don gyaran haikalin Allahnku. Ku yi haka yanzu.” Amma Lawiyawa ba su yi haka nan da nan ba.
6 Entonces el rey envió a Joiada, el principal sacerdote, y le dijo: Por qué no les has dado a los levitas órdenes de que el impuesto fijado por Moisés, el siervo del Señor, y por la reunión de Israel, ordenaron recoger para la Tienda del pacto, debe ser enviada desde Judá y Jerusalén.
Saboda haka sarki ya kira Yehohiyada babban firist ya ce masa, “Me ya sa ba ka bukaci Lawiyawa su kawo harajin da Musa bawan Ubangiji ya ce a biya daga Yahuda da Urushalima da kuma taron Isra’ila domin Tentin Sujada Shaida ba?”
7 Porque la casa del Señor había sido destruida por Atalía, esa mujer malvada, y sus hijos; y todas las cosas santas que habían dado a los baales.
Yanzu’ya’ya muguwar macen nan Ataliya maza sun fasa zuwa cikin haikalin Allah, suka kuma yi amfani da kayayyaki masu tsarki ma wa Ba’al.
8 Así que por orden del rey hicieron un cofre y lo pusieron fuera de la puerta de la casa del Señor.
Bisa ga umarnin sarki, aka yi akwati aka sa a waje, a mashigin haikalin Ubangiji.
9 A través de todo Judá y Jerusalén se envió una orden para que se hiciera un pago al Señor del impuesto que Moisés, el siervo de Dios, había impuesto a Israel en el desierto.
Aka yi umarni a Yahuda da Urushalima cewa ya kamata suka kawo wa Ubangiji harajin da Musa bawan Allah ya bukaci daga Isra’ila a hamada.
10 Y todos los jefes y todas las personas vinieron alegremente y pusieron su dinero en el cofre, hasta llenarlo.
Dukan hafsoshi da dukan mutane suka kawo nasu kuɗin da aka sa musu da farin ciki, suna zuba su cikin akwatin sai da ya cika.
11 Entonces, cuando los levitas llevaron el cofre a los siervos del rey, y vieron que había mucho dinero en él, el escriba del rey y el siervo del sacerdote principal sacaron el dinero y lo volvían a poner en su lugar. Así lo hicieron día a día, y reunieron una gran cantidad de dinero.
Duk sa’ad da Lawiyawa suka fito da akwatin zuwa ga hafsoshin sarki, suka kuma ga cewa akwatin yana da kuɗi mai yawa, sai magatakardan fada da hafsan babban firist su zo su juya kuɗin daga akwatin su mai da shi wurinsa. Sun riƙa yin haka kullum suka tara kuɗi mai yawa.
12 Entonces el rey y Joiada se lo dieron a los responsables de hacer el trabajo en la casa del Señor, y con ello consiguieron que los constructores de paredes y los trabajadores de la madera, el metal, canteros y repararon el templo del Señor.
Sarki da Yehohiyada suka ba da shi ga mutanen da suka yi aikin da ake bukata don haikalin Ubangiji. Suka ɗauki masu gini da kafintoci don su gyara haikalin Ubangiji, da kuma ma’aikatan ƙarafa da tagulla don su gyara haikalin.
13 Entonces los obreros hicieron su trabajo, repararon lo que estaba dañado y repararon la casa de Dios de acuerdo a sus planos y la reforzaron otra vez.
Mutanen da suke lura da aikin natsattsu ne, kuma gyare-gyaren suka ci gaba a ƙarƙashinsu. Suka sāke gina haikalin Allah bisa ga ainihin fasalinsa suka ƙara masa ƙarfi.
14 Y cuando se hizo el trabajo, llevaron el resto del dinero al rey y a Joiada, y se usó para hacer los recipientes para la casa del Señor, todos los recipientes necesarios para las ofrendas, las cucharas y los vasos de oro y plata. Y mientras vivía Joiada, las ofrendas quemadas se ofrecían en la casa del Señor.
Da suka gama, suka kawo sauran kuɗin wa sarki da Yehohiyada, da su ne kuwa aka yi kayayyaki domin hidima da kuma domin hadayun ƙonawa, haka kuma kwanoni da sauran kayayyakin zinariya da azurfa. Muddin Yehohiyada yana raye, aka riƙa kawo hadayun ƙonawa a haikalin Ubangiji.
15 Pero Joiada envejeció y se llenó de días, y llegó a su fin; Tenía ciento treinta años en el momento de su muerte.
Yanzu Yehohiyada ya tsufa kuma cike da shekaru, ya kuwa mutu yana da shekara ɗari da talatin.
16 Y lo enterraron en la ciudad de David, entre los reyes, porque había hecho el bien en Israel con Dios y con su templo.
Aka binne shi tare da sarakuna a cikin Birnin Dawuda, saboda kirkin da ya yi a Isra’ila wa Allah da haikalinsa.
17 Después de la muerte de Joiada, los jefes de Judá vinieron y se postraron sobre sus rostros ante el rey. Entonces el rey les prestó oído.
Bayan mutuwar Yehohiyada, hafsoshin Yahuda suka zo suka yi mubaya’a wa sarki, ya kuma saurare su.
18 Y dejaron la casa del Señor Dios de sus padres, y se convirtieron en adoradores de los pilares de madera y de las imágenes; y debido a este pecado de ellos, vino ira sobre Judá y Jerusalén.
Suka yashe haikalin Ubangiji Allah na kakanninsu, suka bauta wa ginshiƙan Ashera da kuma gumaka. Saboda laifinsu, fushin Allah ya sauko a kan Yahuda da Urushalima.
19 Y el Señor les envió profetas para que regresaran a él; y dieron testimonio contra ellos, pero no quisieron escuchar.
Ko da yake Ubangiji ya aiki annabawa zuwa wurin mutane don su dawo da su gare shi, kuma ko da yake sun ba da shaida a kansu, ba su saurara ba.
20 Entonces vino el espíritu de Dios sobre Zacarías, el hijo del sacerdote Joiada, y levantándose delante del pueblo, les dijo: Dios ha dicho: ¿Por qué vas contra las órdenes del Señor? todo te va mal? porque han abandonado al Señor, él te ha abandonará.
Sai Ruhun Allah ya sauko a kan Zakariya ɗan Yehohiyada firist. Ya tsaya a gaban mutane ya ce, “Ga abin da Allah ya ce, ‘Me ya sa ba ku yi biyayya da umarnan Ubangiji ba? Ba za ku yi nasara ba. Domin kun yashe Ubangiji, shi ma ya yashe ku.’”
21 Pero cuando hicieron un plan secreto contra él, fue apedreado con piedras, por orden del rey, en el atrio exterior del templo del Señor.
Amma suka yi masa maƙarƙashiya, kuma ta wurin umarnin sarki suka jajjefe shi da duwatsu har ya mutu a filin haikalin Ubangiji.
22 Entonces el rey Joás no tuvo en cuenta lo bueno que había sido su padre Joiada, sino que mató a su hijo Zacarías, Y en la hora de su muerte, dijo: ¡Que el Señor lo vea y reciba el pago!
Sarki Yowash bai tuna da alherin da Yehohiyada mahaifin Zakariya ya nuna masa ba, sai ya kashe ɗansa, wanda ya ce yayinda yake mutuwa, “Bari Ubangiji yă dubi wannan yă kuma sāka maka.”
23 Ahora, en la primavera, el ejército de los sirios se alzó contra él; vinieron contra Judá y Jerusalén, matando a todos los grandes hombres del pueblo y enviando todos los bienes que tomaron de ellos al rey de Damasco.
Da shekara ta kewaye, mayaƙan Aram suka yi gāba da Yowash suka kai hari wa Yahuda da Urushalima suka kuma kashe dukan shugabannin mutane, suka aika da dukan ganima zuwa ga sarkinsu a Damaskus.
24 Porque aunque el ejército de Siria era muy pequeño, el Señor puso en sus manos un ejército muy grande, porque habían abandonado al Señor, el Dios de sus antepasados. Así ejecutaron castigo contra Joás.
Ko da yake mayaƙan Arameyawa sun zo da mutane kaɗan kawai, Ubangiji ya sa suka ci nasara a kan sojojin Yahuda mafi yawa, don mutanen Yahuda sun rabu da Ubangiji Allah na kakanninsu, aka kuma hukunta Yowash.
25 Y cuando ellos se alejaron de él porque estaba gravemente herido, sus siervos hicieron un plan secreto contra él por la sangre del hijo del sacerdote Joiada, y lo mataron en su cama; y lo enterraron en la ciudad de David, pero no en el panteón de los reyes.
Sa’ad da Arameyawa suka janye, suka bar Yowash da mummunan rauni. Hafsoshinsa suka haɗa baki a kansa saboda kisan ɗan Yehohiyada firist da ya yi, suka kashe shi a kan gadonsa. Ta haka ya mutu aka kuma binne shi makabartan sarakuna.
26 Los que hicieron planes contra él fueron Zabad, el hijo de Simeat, un amonita, y Jozaba, el hijo de Simrit, un moabita.
Waɗanda suka haɗa bakin kuwa su ne Zabad ɗan Shimeyat wata mutuniyar Ammon da Yehozabad ɗan Shimrit wata mutuniyar Mowab.
27 Ahora, la historia de sus hijos, y todas las palabras que el profeta dijo contra él, y la edificación de la casa del Señor, están registradas en el libro de los reyes. Y su hijo Amasías se hizo rey en su lugar.
Labarin’ya’yansa maza, annabce-annabce masu yawa game da shi, da tarihin gyaran haikalin Allah suna a rubuce a rubuce-rubuce a littafin sarakuna. Amaziya ɗansa kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.