< 1 Samuel 24 >

1 Cuando Saúl regresó de pelear contra los filisteos, se le dieron noticias de que David estaba en él desierto de En-Gedi.
Bayan da Shawulu ya komo daga fafaran Filistiyawa, sai aka gaya masa cewa, “Dawuda yana can a Jejin En Gedi.”
2 Luego Saúl sacó a tres mil de los mejores hombres de todo Israel, y fue en busca de David y sus hombres sobre las rocas de las cabras montesas.
Saboda haka Shawulu ya zaɓi mutum dubu uku daga cikin dukan Isra’ila, suka fita neman Dawuda da mutanensa kusa da Duwatsun Awakin Jeji.
3 Y en el camino llegó a un lugar donde se guardaban las ovejas, donde había una cueva; y Saúl entró para hacer sus necesidades. Ahora David y sus hombres estaban en la parte más profunda de la cueva.
Da Shawulu ya isa inda ake ajiye garken tumaki a bakin hanya inda akwai kogo, sai ya shiga ciki kogon don yă yi bayan gari. Dawuda da mutanensa kuwa suna can zaune a ƙurewar kogon.
4 Entonces los hombres de David le dijeron: Ahora es el momento en que el Señor te dice: entregaré a tu enemigo en tus manos para hacer con él lo que te parezca bien. Entonces David, levantándose, tomó el manto de Saúl en su mano, cortándole la esquina sin que lo supiera.
Mutanen Dawuda suka ce, wannan rana ce Ubangiji ya yi magana ya ce maka, “Zan ba da maƙiyinka a hannunka domin ka yi abin da ka ga dama da shi.” Sai Dawuda ya tashi a hankali ya je ya yanke shafin rigar Shawulu.
5 Y luego, después, David le remordió la conciencia y se arrepintió de haber cortado el manto de Saúl.
Daga baya Dawuda ya damu domin ya yanke shafin rigar Shawulu.
6 Y David dijo a sus hombres: Ante el Señor, nunca se diga que mi mano se levantó contra mi señor, el hombre escogido del Señor, porque el aceite santo del Señor fue puesto sobre él.
Ya ce wa mutanensa, “Ubangiji yă sawwaƙe in yi abu haka ga shugabana da Ubangiji ya shafe, ko in ɗaga hannuna in kashe shi, gama shi shafaffe ne na Ubangiji.”
7 Entonces, con estas palabras, David retuvo a sus sirvientes y no les permitió atacar a Saúl. Y Saúl se levantó y siguió su camino.
Da wannan magana Dawuda ya kwaɓi mutanensa, bai yarda su fāɗa wa Shawulu ba. Shawulu kuwa ya bar kogon ya yi tafiyarsa.
8 Después de esto, David salió de la cueva, y clamando a Saúl, dijo: Señor mío, el rey. Y cuando Saúl le devolvió la mirada, David se inclinó hasta el suelo y le dio honor.
Daga baya Dawuda ya fita daga kogon sai ya kira Shawulu ya ce, “Ranka yă daɗe, sarki!” Da Shawulu ya waiwaya, sai Dawuda ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
9 Entonces David dijo a Saúl: ¿Por qué prestas atención a los que dicen que es mi deseo hacerte mal?
Ya ce wa Shawulu, “Me ya sa kake saurari mutanen da suke cewa, ‘Dawuda ya dāge yă cuce ka’?
10 ¡Mira! has visto hoy cómo el Señor te entregó en mis manos incluso ahora en la cueva, y algunos dijeron que te matara, pero tuve compasión de ti, porque dije, nunca se levantará mi mano contra mi señor, que es él escogido del Señor, ha sido ungido con el aceite santo.
Yau ka ga da idonka yadda Ubangiji ya bashe ka a hannuna a cikin kogon nan. Waɗansu sun ce mini in kashe ka, amma na bar ka, na ce, ‘Ba zan sa hannuna a kan shugabana ba, gama shi shafaffe ne na Ubangiji.’
11 Y mira, padre mío, ve la esquina de tu túnica en mi mano: porque el hecho de que corte la falda de tu túnica y no te maté es prueba de que no tengo ningún propósito malo, y yo no hecho ningún mal, sin embargo tú me estás buscando para matarme.
Babana, duba, ga shafin rigarka a hannuna, na yanke shafin rigarka amma ban kashe ka ba. Yanzu ka gane ka kuma sani cewa ba ni da laifin aikata kome ko tayarwa, ban yi maka laifi ba, amma kana farautar raina.
12 Que el Señor sea juez entre tú yo, y que el Señor me otorgue mis derechos contra ti, pero mi mano nunca será levantada contra ti.
Ubangiji zai shari’anta tsakanina da kai. Ubangiji zai sāka mini laifin da ka yi mini, amma ni kam ba zan taɓa ka ba.
13 Hay un viejo dicho: del malvado viene el mal, pero mi mano nunca será levantada contra ti.
Kamar yadda karin maganan nan na dā ya ce, ‘Daga cikin masu mugunta, mugunta ke fitowa,’ hannuna dai ba zai taɓa ka ba.
14 ¿Después de quién salió el rey de Israel? para quien estas buscando Por un perro muerto, un insecto.
“Wane ne sarkin Isra’ila, ka fito kake bi? Wa kake kora? Kana bin mataccen kare ko kuɗin cizo?
15 Dejemos que el Señor sea juez y tome una decisión entre tú y yo, y vea y apoye mi causa, y evite que caiga en tus manos.
Ubangiji yă zama alƙali, yă yi shari’a tsakanina da kai, bari Ubangiji yă duba, yă tsaya mini, yă nuna ba ni da laifi.”
16 Cuando David le dijo estas palabras a Saúl, Saúl dijo: ¿Esta es tu voz, David, hijo mío? Y Saúl fue vencido por el llanto.
Da Dawuda ya gama wannan magana, sai Shawulu ya ce, “Muryarka ke nan ɗana Dawuda?” Sai ya fasa da kuka.
17 Y él le dijo a David: Tienes razón y yo estoy equivocado, porque me has devuelto el bien, pero yo te he dado el mal.
Ya ce, “Ka fi ni gaskiya, ka yi mini alheri, ni kuwa na yi maka mugunta.
18 Y me has dejado claro cuán bueno me has sido hoy, porque cuando el Señor me entregó en tus manos, no me hiciste morir.
Ga shi yanzu ka faɗa mini alherin da ka yi mini. Ubangiji ya bashe ni a hannunka amma ba ka kashe ni ba.
19 Si un hombre se encuentra con su enemigo, ¿lo dejará escapar a salvo? para que seas recompensado por el Señor por lo que has hecho por mí hoy.
In mutum ya sami maƙiyinsa, zai bar shi yă tafi lafiya ba tare da yin masa rauni ba? Ubangiji yă sāka maka, gama ka nuna mini alheri a yau.
20 Y ahora estoy seguro de que serás rey, y que el reino de Israel se fortalecerá bajo tu autoridad.
Na sani tabbatacce za ka zama sarki. Masarautar Isra’ila za tă kahu a hannunka.
21 Dame tu juramento por el Señor, que no acabes con mi simiente después de mí ni dejes que mi nombre sea separado de la familia de mi padre.
Yanzu ka rantse mini da Ubangiji cewa ba za ka hallaka zuriyarta ko ka share sunana daga iyalin mahaifina ba.”
22 Y David juró a Saúl. Y Saúl volvió a su casa; pero David y sus hombres subieron a su fortaleza.
Sai Dawuda ya rantse wa Shawulu. Sa’an nan Shawulu ya koma gida, amma Dawuda da mutanensa suka haura zuwa wurin ɓuya.

< 1 Samuel 24 >