< 1 Pedro 5 >

1 Yo, que soy anciano como ellos de la iglesia, y un testigo de los sufrimientos de Cristo, teniendo mi parte en la gloria venidera, ruego a los ancianos de la congregación que están entre ustedes.
Zuwa ga dattawan da suke cikinku, ina roƙo a matsayin ɗan’uwanku dattijo, mashaidin shan wahalar Kiristi wanda kuma shi ma zai sami rabo cikin ɗaukakar da za a bayyana.
2 Vigilen al rebaño de Dios que está bajo su cuidado, usando su autoridad, no como forzado a hacerlo, pero con mucho gusto; como Dios quiere y no por obligación ni por ganancias inmundas, realicen su trabajo de buena gana;
Ku zama makiyayan garken Allah da yake a ƙarƙashin kulawarku, kuna hidima kamar masu kula, ba kan dole ba, sai dai da yardar rai, yadda Allah yake so ku zama; ban da kwaɗayin kuɗi, sai dai marmarin yin hidima;
3 No como señores y dueños de los que están a su cuidado, sino haciéndose ejemplos del rebaño.
ban da nuna iko a kan waɗanda aka danƙa muku amana, sai dai ku zama gurbi ga garken.
4 Y a la venida del Pastor principal de las ovejas, se te dará la corona de gloria, una corona que jamás se marchitará.
Sa’ad da kuwa Babban Makiyayin ya bayyana, za ku karɓi rawanin ɗaukaka marar koɗewa.
5 Y de la misma manera, jóvenes sométanse a los más viejos. Y todos ustedes, sumisos unos con otros y sean revestidos de humildad: porque Dios es enemigo del orgulloso, pero da gracia a los humildes.
Samari, ku ma, ku yi biyayya ga waɗanda suka girme ku. Dukanku, ku yafa sauƙinkai ga juna, domin, “Allah yana gāba da mai girman kai, amma yakan yi alheri ga mai sauƙinkai.”
6 Por esto, humíllense bajo la mano fuerte de Dios, para que cuando llegue el momento, sean enaltecidos;
Saboda haka, ku ƙasƙantar da kanku a ƙarƙashin hannun Allah mai ƙarfi, don yă ɗaukaka ku a lokacin da ya ga dama.
7 Poniendo todas sus preocupaciones mundanas en él, porque él cuida de ustedes.
Ku danƙa masa dukan damuwarku, domin shi ne yake lura da ku.
8 Sean prudentes y manténganse despiertos; el Maligno, que está contra ustedes, anda alrededor como un león con la boca abierta en busca de comida;
Ku zama masu kamunkai, ku kuma zauna a faɗake. Abokin gābanku, Iblis yana kewayewa kamar zaki mai ruri, yana neman wanda zai cinye.
9 Resístanlo séan fuerte en su fe, sabiendo que tus hermanos que están en el mundo sufren los mismos problemas.
Ku yi tsayayya da shi, kuna tsayawa daram cikin bangaskiya, domin kun san cewa’yan’uwanku ko’ina a duniya suna shan irin wahalolin nan.
10 Y después de haber sufrido dolor por un tiempo, el Dios de toda gracia que nos ha dado parte en su gloria eterna por medio de Cristo Jesús, él mismo les dará fortaleza y apoyo, y los perfeccionará en todo lo bueno; (aiōnios g166)
Allah mai dukan alheri, wanda ya kira ku ga madawwamiyar ɗaukaka cikin Kiristi, bayan kun sha wahala na ɗan lokaci, shi da kansa zai raya ku, yă kuma sa ku yi ƙarfi, ku kahu, ku kuma tsaya daram. (aiōnios g166)
11 A sea el poder y la gloria para siempre. Que así sea. (aiōn g165)
Gare shi bari iko yă tabbata har abada abadin. Amin. (aiōn g165)
12 Les he enviado esta breve carta de Silvano, un verdadero hermano, en mi opinión; exhortándoles dando testimonio de que esta es la verdadera gracia de Dios; sigan firmes.
Da taimakon Sila, wanda na ɗauka a matsayin ɗan’uwa mai aminci, na rubuta muku a taƙaice, ina ƙarfafa ku ina kuma shaida muku cewa wannan shi ne alherin Allah na gaske. Ku tsaya daram a cikinsa.
13 La iglesia que está en Babilonia, que tiene una parte contigo en el propósito de Dios, te envía saludos; y mi hijo Marcos también.
Ita wadda take a Babilon, zaɓaɓɓiya tare da ku, tana gaishe ku, haka ma ɗana Markus.
14 Saludense unos a otros con un beso de amor. La paz sea para todos ustedes que están en Cristo Jesús.
Ku gai da juna da sumbar ƙauna. Salama gare ku duka da kuke cikin Kiristi.

< 1 Pedro 5 >