< 1 Reyes 13 >

1 Entonces un hombre de Dios vino de Judá por orden del Señor a Betel, donde Jeroboam estaba junto al altar, quemando ofrendas.
Bisa ga umarnin Ubangiji, sai wani mutumin Allah ya zo daga Yahuda zuwa Betel, yayinda Yerobowam yake tsaye kusa da bagade don yă miƙa hadaya.
2 Por orden del Señor, clamó contra el altar, diciendo: Oh altar, altar, el Señor ha dicho: De la simiente de David vendrá un niño, llamado Josías y sobre ti él sacrificará a los sacerdotes de los lugares altos, que están quemando ofrendas en ti, y los huesos de los hombres serán quemados sobre ti.
Sai mutumin Allah ya tā da murya a kan bagade bisa ga umarnin Ubangiji ya ce, “Ya bagade, bagade! Ubangiji ya ce, ‘Za a haifi ɗa mai suna Yosiya wa gidan Dawuda. A kanka zai miƙa firistoci na masujadai kan tuddai masu miƙa hadayu a nan, za a kuma ƙone ƙasusuwan mutane a kanka.’”
3 El mismo día les dio una señal, diciendo: Esta es la señal que el Señor ha dado: Mira, el altar se romperá y los residuos quemados sobre él se esparcirá.
A wannan rana mutumin Allah ya ba da alama, “Ga alamar da Ubangiji ya furta. Wannan bagade zai tsage yă rabu kashi biyu, tokar da yake a kansa za tă zuba a ƙasa.”
4 Entonces el rey, al oír al hombre de Dios clamando contra el altar en Betel, extendió su mano del altar, diciendo: Hazlo prisionero. Y su mano, extendida contra él, quedó tiesa y no tuvo poder para moverla.
Sa’ad da Yerobowam ya ji abin da mutumin Allah ya tā da murya ya faɗa game da bagaden Betel, sai ya miƙa hannunsa daga bagaden ya ce, “Ku kama shi!” Amma sai hannun da ya miƙa ya yanƙwane, har bai iya janye shi ba.
5 Y se rompió el altar y se esparcieron sobre ella los residuos quemados; esta fue la señal que el hombre de Dios había dado por la palabra del Señor.
Haka ma, bagaden ya rabu, tokarsa kuma ya zuba, bisa ga alamar da mutumin Allah ya bayar, ta wurin kalmar Ubangiji.
6 Entonces el rey respondió y dijo al hombre de Dios: Ahora ora por la gracia del Señor tu Dios, y por mí, para que mi mano esté bien. Y en respuesta a la oración del hombre de Dios, la mano del rey se recuperó, como antes.
Sai sarki ya ce wa mutumin Allah, “Ka roƙi Ubangiji Allahnka, ka kuma yi addu’a domina don hannuna ya warke.” Saboda haka mutumin Allah ya yi roƙo ga Ubangiji, hannun sarki kuwa ya warke, ya kuma zama kamar yadda yake a dā.
7 Y el rey dijo al hombre de Dios: Ven conmigo a mi casa a comer y descansar, y te daré una recompensa.
Sai sarki ya ce wa mutumin Allah, “Zo gida tare da ni, ka sami wani abu ka ci, zan kuwa yi maka kyauta.”
8 Pero el hombre de Dios dijo al rey: Aunque me dieras la mitad de todo lo que tienes, no entraría contigo, y no tomaría comida ni un poco de agua en este lugar;
Amma mutumin Allah ya amsa wa sarki, “Ko da za ka ba rabin mallakarka, ba zan tafi tare da kai ba, ba kuwa zan ci abinci, ko in sha ruwa a can ba.
9 Porque así me ordenó la palabra del Señor, que dijo: No debes comer ni beber agua, ni debes volver por el camino que viniste.
Gama an umarce ni ta wurin kalmar Ubangiji, aka ce, ‘Kada ka ci abinci, ko ka sha ruwa, ko ka koma ta hanyar da ka zo.’”
10 Y se fue por otro camino, y no por la forma en que llegó a Betel.
Saboda haka ya ɗauki wata hanya, bai kuwa koma ta hanyar da ya zo Betel ba.
11 Ahora había un viejo profeta viviendo en Betel; y uno de sus hijos vino y le dio la noticia de todo lo que el hombre de Dios había hecho ese día en Betel, y le contaron a su padre las palabras que había dicho al rey.
To, fa, akwai wani tsohon annabi yana zama a Betel, wanda’ya’yansa suka zo suka faɗa masa dukan abin da mutumin Allah ya yi a can, a ranar. Suka kuma faɗa wa mahaifinsu abin da ya faɗa wa sarki.
12 Entonces su padre les dijo: ¿Por qué camino se fue? Ahora sus hijos habían visto en qué dirección se había ido el hombre de Dios que venía de Judá.
Mahaifinsu ya tambaye su ya ce, “Wace hanya ce ya bi?” Sai’ya’yansa suka nuna masa hanyar da mutumin Allah daga Yahuda ya bi.
13 Entonces el profeta dijo a sus hijos: ensíllenme un asno. Así que ellos ensillaron un asno, y él se subió,
Sai ya ce wa’ya’yansa, “Ku yi wa jakina shimfiɗa.” Da suka yi wa jakin shimfiɗa, sai ya hau.
14 Fue tras el hombre de Dios, y subió con él mientras estaba sentado debajo de un roble. Y él le dijo: ¿Eres tú el hombre de Dios que vino de Judá? Y él dijo: Yo soy.
Ya bi bayan mutumin Allah. Ya same shi yana zama a ƙarƙashin itace oak, sai ya tambaye shi ya ce, “Kai ne mutumin Allah wanda ya zo daga Yahuda?” Ya amsa, “Ni ne.”
15 Entonces le dijo: Ven conmigo a la casa y come.
Saboda haka annabin ya ce masa, “Zo gida tare da ni ka ci abinci.”
16 Pero él dijo: No puedo volver contigo ni entrar en tu casa; y no llevaré comida ni un trago de agua contigo en este lugar;
Mutumin Allah ya ce, “Ba zan koma tare da kai ba, ko in ci abinci, ko in sha ruwa tare da kai a can ba.
17 Porque el Señor me dijo: No debes llevar comida ni agua allí, ni regresar por el camino que viniste.
An faɗa mini ta wurin maganar Ubangiji, ‘Kada ka ci abinci, ko ka sha ruwa a can, ko ka koma ta hanyar da ka zo.’”
18 Entonces él le dijo: Yo soy profeta como tú; Y un ángel me dijo por la palabra del Señor: Llévalo contigo y dale de comer y agua. Pero él le dijo palabras falsas.
Sai annabin ya amsa, “Ni ma annabi ne, kamar ka. Kuma mala’ika ya ce mini ta wurin kalmar Ubangiji, ‘Dawo da shi zuwa gidanka saboda yă ci abinci, yă kuma sha ruwa.’” (Amma yana masa ƙarya ne.)
19 Volvió con él, y comió en su casa y bebió agua.
Sai mutumin Allah ya koma tare da shi ya kuma ci ya sha a gidansa.
20 Pero mientras estaban sentados a la mesa, vino la palabra del Señor al profeta que lo había hecho volver;
Yayinda suke zaune a teburi, sai maganar Ubangiji ta zo wa tsohon annabin da ya dawo da mutumin Allah.
21 Y clamando al hombre de Dios que vino de Judá, dijo: El Señor dice: Has ido en contra de la voz del Señor, y no has hecho lo que el Señor te ordenó,
Sai tsohon annabin ya tā da murya wa mutumin Allah wanda ya zo daga Yahuda, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka ƙazantar da maganar Ubangiji, ba ka kuma kiyaye umarnin Ubangiji Allahnka ba.
22 Pero han regresado, y han tomado comida y agua en este lugar donde él dijo que no debían tomar comida ni agua; tu cuerpo muerto no descansará con tus padres.
Ka dawo ka ci abinci, ka kuma sha ruwa a wurin da na faɗa maka kada ka ci, ko ka sha. Saboda haka ba za a binne jikinka a kabarin kakanninka ba.’”
23 Después de la comida, preparó el asno para él, para el profeta a quien había devuelto.
Sa’ad da mutumin Allah ya gama ci da sha, sai annabin da ya dawo da shi ya yi wa jakin mutumin Allah shimfiɗa.
24 Y siguió su camino; pero en el camino, un león vino corriendo hacia él y lo mató; y su cuerpo muerto estaba tendido en el camino con el asno a su lado, y el león estaba allí junto al cuerpo.
Yayinda yake kan hanyarsa, sai wani zaki ya sadu da shi ya kashe shi, aka kuma jefar da jikinsa a kan hanya, jakin da zakin suka tsaya kusa da gawar.
25 Al pasar algunos hombres, vieron el cuerpo tendido en el camino con el león a su lado; y vinieron y dieron noticias de ello en la ciudad donde vivía el viejo profeta.
Waɗansu mutane masu wucewa suka ga an yar da gawar a can, zaki yana tsaye kusa da gawar, sai suka tafi suka ba da labarin a birni inda tsohon annabin nan yake zama.
26 Entonces el profeta que lo había hecho volver, al oírlo, dijo: Es el hombre de Dios, que fue en contra de la palabra del Señor; es por eso que el Señor lo ha entregado al león para que sea herido de muerte, como dijo el Señor.
Sa’ad da annabin da ya dawo da mutumin Allah ya ji, sai ya ce, “Mutumin Allah ne, wanda ya ƙazantar da maganar Ubangiji. Ubangiji ya bashe shi ga zaki, wanda ya yayyage shi ya kuma kashe shi, kamar yadda maganar Ubangiji ta gargaɗe shi.”
27 Y dijo a sus hijos: Prepara el asno para mí. Y así lo hicieron.
Sai annabin ya ce wa’ya’yansa, “Ku yi wa jakina shimfiɗa.” Sai suka yi.
28 Luego fue y vio el cuerpo muerto tendido en el camino con el asno y el león a su lado: el león no había tomado el cuerpo para su comida ni había hecho ningún daño al asno.
Sai ya fita ya sami an jefar da gawar a hanya, jakin da zakin suna tsaye kusa da shi. Zakin bai ci gawar ko yă yayyage jakin ba.
29 Entonces el profeta tomó el cuerpo del hombre de Dios, lo puso sobre el asno y lo tomó de vuelta; y él vino al pueblo a enterrar él cuerpo y estar de luto.
Saboda haka annabin ya ɗauki gawar mutumin Allah, ya shimfiɗa shi a kan jaki, ya koma da shi cikin birninsa don yă yi makokinsa yă kuma binne shi.
30 Y enterró el cuerpo en él lugar preparado para él, llorando y lamentándose, diciendo: ¡Oh hermano mío!
Sai ya kwantar da gawar a kabarinsa, suka yi makoki a kansa, ya kuma ce, “Ayya, abokina!”
31 Y después de haberlo enterrado, dijo a sus hijos: Cuando yo muera, debes enterrarme con el cuerpo de este hombre de Dios, y ponerme junto a sus huesos para que mis huesos se mantengan con sus huesos.
Bayan an binne shi, sai ya ce wa’ya’yansa, “Sa’ad da na mutu, ku binne ni a kabarin da aka binne mutumin Allah; ku kwantar da ƙasusuwana kusa da ƙasusuwansa.
32 Porque ciertamente se producirá el clamor que hizo por la palabra del Señor contra el altar en Betel y contra todas las casas de los lugares altos en los pueblos de Samaria.
Gama annabcin da ya yi ta maganar Ubangiji gāba da bagaden da yake cikin Betel da kuma wuraren sujada a tuddan da suke a biranen Samariya, ba shakka zai cika.”
33 Después de esto, Jeroboam, sin apartarse de sus malos caminos, hizo sacerdotes para sus altares de entre todas las personas; hizo un sacerdote a quien él deseara, para que pudiera haber sacerdotes de los lugares altos.
Har ma bayan wannan, Yerobowam bai canja daga mugayen hanyoyinsa ba, amma ya ƙara naɗa firistoci domin masujadai da suke kan tuddai daga kowane irin mutane. Duk wanda ya so yă zama firist sai yă naɗa shi don aiki a masujadai da suke kan tuddai.
34 Y esto se convirtió en pecado en la familia de Jeroboam, causando que fuera cortado y enviado a la destrucción de la faz de la tierra.
Wannan ne zunubin gidan Yerobowam da ya kai ga fāɗuwarsa da kuma hallakarsa daga fuskar duniya.

< 1 Reyes 13 >