< 1 Corintios 11 >

1 Siganme, así como yo sigo a Cristo.
Ku bi gurbina, kamar yadda ni nake bin gurbin Kiristi.
2 Ahora me complace ver que me tienen en la memoria en todas las cosas, y siguen las enseñanzas que les enseñe.
Ina yabonku saboda kuna tunawa da ni a cikin kowane abu, kuna kuma riƙe da koyarwar, yadda na ba ku.
3 Pero es importante que tengan en cuenta este hecho, que la cabeza de cada hombre es Cristo; y la cabeza de la mujer es el hombre, y la cabeza de Cristo es Dios.
To, ina so ku gane cewa shugaban kowane namiji Kiristi ne, shugaban mace namiji ne, shugaban Kiristi kuma Allah ne.
4 Todo hombre que toma parte en la oración, o que enseña como profeta, con la cabeza cubierta, deshonra al que es su cabeza.
Kowane namijin da ya yi addu’a ko annabci da kansa a rufe ya jawo kunya wa kansa.
5 Pero cada mujer que que ora o profetiza lo hace con la cabeza descubierta, deshonra su cabeza, porque es lo mismo que si le cortaran el cabello.
Duk macen da ta yi addu’a ko annabci da kanta a buɗe kuwa ta rena kanta, ya zama kamar an aske kanta ke nan.
6 Porque si una mujer no está encubierta, que se corte su cabello; pero si es una vergüenza para una mujer cortarse el pelo, que se la cubra.
In mace ba ta so tă rufe kanta, to, sai tă aske gashinta; in kuwa abin kunya ne mace tă yanke ko tă aske gashinta, to, sai tă rufe kanta.
7 Porque no es justo que un hombre se cubra la cabeza, porque él es imagen y gloria de Dios; pero la mujer es la gloria del hombre.
Namiji kuwa bai kamata ya rufe kansa ba, da yake shi kamannin Allah ne, da kuma darajar Allah, amma mace dai, darajar namiji ne.
8 Porque el hombre no vino de la mujer, sino la mujer del hombre.
Gama namiji bai fito daga mace ba, sai dai mace ce ta fito daga namiji.
9 Y el hombre no fue creado por causa de la mujer, sino la mujer por causa del hombre.
Ba a kuma halicci namiji don mace ba, sai dai mace don namiji.
10 Por esta razón, es correcto que la mujer tenga una señal de autoridad en su cabeza, debido a los ángeles.
Don haka, saboda wannan, da kuma saboda mala’iku, dole mace ta ɗaura wani abu a kanta.
11 Pero la mujer no está separada del hombre, y el hombre no está separado de la mujer en el Señor.
Duk da haka a cikin Ubangiji, mace ba a rabe take da namiji ba, namiji kuma ba a rabe yake da mace ba.
12 Porque como la mujer fue formada del hombre, así el varón viene de la mujer; pero todas las cosas vienen de Dios.
Kamar yadda mace ta fito daga namiji, haka kuma aka haifi namiji ta wurin mace. Sai dai kowane abu daga Allah yake.
13 Sean ustedes mismos los jueces de la pregunta: ¿le parece correcto que una mujer ore sin cubrirse la cabeza?
Ku kanku duba mana. Ya yi kyau mace tă yi addu’a ga Allah da kanta a buɗe?
14 La naturaleza misma nos enseña que es deshonroso que él hombre se deje crecer el pelo.
Kai, yadda halitta take ma, ai, ta koya muku cewa in namiji yana da dogon gashi, abin kunya ne a gare shi,
15 Pero si una mujer tiene pelo largo, es una gloria para ella, porque se le ha dado el pelo como cubierta.
amma in mace tana da dogon gashi, ai, daraja ce a gare ta. Gama an ba ta dogon gashi saboda rufe kanta ne.
16 Pero si algún hombre quiere ser contencioso, esta no es nuestra manera de hacer las cosas, y no se hace en las iglesias de Dios.
In akwai mai gardama da wannan, to, mu dai ba mu da wata al’ada, haka ma ikkilisiyoyin Allah.
17 Pero al darles esta orden, hay una cosa que no me agrada: es que cuando se juntan no es para mejor sino para peor.
Game da umarnan nan dai, ban yaba muku ba, domin taruwarku ba ta kirki ba ce, ɓarna ce.
18 Antes que nada, me viene a la mente que cuando se reúnen en la iglesia, hay divisiones entre ustedes, y considero que la declaración es verdadera en parte.
Da farko dai, na ji cewa sa’ad da kuka taru a matsayin ikkilisiya, akwai tsattsaguwa a tsakaninku, har na fara yarda da zancen.
19 Porque las divisiones son necesarias entre ustedes, para que aquellos que tienen la aprobación de Dios sean claramente vistos entre ustedes.
Ba shakka dole a sami bambanci a tsakaninku don a nuna wa Allah ya amince da shi a cikinku.
20 Pero ahora, cuando se unen, no es posible tomar la santa comida del Señor:
Sa’ad da kuka taru, ba Cimar Ubangiji kuke ci ba,
21 Porque cuando tomas tu comida, todos toman su comida antes que la otra; y uno no tiene suficiente comida, y otros hasta se emborrachan.
gama yayinda kuke ci, kowa yakan ci gaba ba tare da jiran wani ba. Wani yă zauna da yunwa, wani kuma yă bugu.
22 ¿Qué? ¿No tienen sus casas para beber y comer? o no tienes respeto por la iglesia de Dios, avergonzando a los pobres? ¿Qué voy a decirles? ¿Debo felicitarlos? ciertamente no.
Kai, ba ku da gidajen da za ku ci ku sha ne? Ko dai kun rena ikkilisiyar Allah ne, kuna kuma wulaƙanta waɗanda ba su da kome? Me zan ce muku? In yabe ku ne game da wannan? A’a, ko kaɗan!
23 Porque del Señor recibí esta enseñanza y lo que les he enseñado, que el Señor Jesús, en la noche en que Judas lo traicionó, tomó pan,
Gama abin da na karɓa daga wurin Ubangiji shi ne nake ba ku. Ubangiji Yesu, a daren da aka bashe shi, ya ɗauki burodi,
24 y cuando se quebró con un acto de alabanza, él dijo: Este es mi cuerpo, que por ustedes es partido; haz esto en memoria de mí.
bayan ya yi godiya, sai ya kakkarya ya ce, “Wannan jikina ne, wanda yake dominku, ku yi wannan don tunawa da ni.”
25 De la misma manera, con la copa, después de la comida, dijo: Esta copa es el nuevo testamento en mi sangre: haz esto, siempre que lo beban, en memoria de mí.
Haka kuma bayan cimar, ya ɗauki kwaf, yana cewa, “Wannan kwaf ne sabon alkawari a jinina; ku yi wannan, a duk sa’ad da kuke sha, don tunawa da ni.”
26 Porque cada vez que toman el pan y el cáliz, das testimonio de la muerte del Señor hasta que él venga.
Gama a duk sa’ad da kuke cin wannan burodi, kuke kuma sha daga wannan kwaf, kuna shelar mutuwar Ubangiji ne har yă dawo.
27 Si, entonces, alguien toma el pan o la copa del Señor en el espíritu equivocado, él será responsable del cuerpo y la sangre del Señor.
Saboda haka, duk wanda ya ci burodin ko ya sha daga kwaf na Ubangiji da rashin cancanta, ya yi laifin wulaƙanta jiki da jinin Ubangiji ke nan.
28 Pero que nadie tome del pan y la copa sin probarse a sí mismo.
Dole kowa yă bincike kansa kafin yă ci burodin yă kuma sha daga kwaf ɗin.
29 Porque un hombre se pone en peligro, si participa en la comida santa sin ser consciente de que es el cuerpo del Señor.
Gama duk wanda ya ci ya kuma sha ba tare da fahimtar jikin Ubangiji ba, ya ci ya kuma sha wa kansa hukunci ne.
30 Por esta causa, algunos de ustedes son débiles y enfermos, y un número está muerto.
Shi ya sa da yawa a cikinku ba su da ƙarfi, suna kuma da rashin lafiya, waɗansunku kuma sun riga sun yi barci.
31 Pero si fuéramos verdaderos jueces de nosotros mismos, el castigo no nos vendría encima.
Amma in da za mu auna kanmu sosai, da ba za mu shiga irin hukuncin nan ba.
32 Pero si el castigo llega, es enviado por el Señor, para que podamos estar a salvo cuando el mundo sea juzgado.
Duk da haka sa’ad da Ubangiji ya hukunta mu, ana yin mana horo ne don kada a ƙarshe a hallaka mu tare da duniya.
33 Así que, hermanos míos, cuando se unan a la santa comida del Señor, espérense unos a otros.
Saboda haka’yan’uwana, sa’ad da kuka taru don ci, ku jira juna.
34 Si alguno tiene hambre, para que Dios no tenga que castigarlos por esa clase de reuniones Y el resto lo pondré en orden cuando vaya a verlos.
In wani yana jin yunwa, sai yă ci abinci a gida, saboda in kuka taru kada yă jawo hukunci. Sa’ad da na zo kuma zan ba da ƙarin umarnai.

< 1 Corintios 11 >