< 1 Crónicas 19 >
1 Después de esto sucedió que la muerte llegó a Nahas, el rey de los hijos de Amón, y su hijo se convirtió en rey en su lugar.
Ana nan, sai Nahash sarkin Ammonawa ya mutu, sai ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
2 Y dijo David: Seré amigo de Hanun, el hijo de Nahas, porque su padre era amigo mío. Entonces David le envió hombres para que le dieran palabras de consuelo a causa de su padre. Y los siervos de David fueron a Hanun, a la tierra de los hijos de Amón, ofreciéndole consuelo.
Dawuda ya yi tunani, “Zan nuna jinƙai ga Hanun ɗan Nahash, domin mahaifinsa ya nuna alheri gare ni.” Saboda haka Dawuda ya aika da tawaga don yă yi wa Hanun ta’aziyya game da mahaifinsa. Sa’ad da mutanen Dawuda suka iso wurin Hanun a ƙasar Ammonawa don su ta’azantar da shi,
3 Pero los jefes de los hijos de Amón le dijeron a Hanun: ¿Te parece que David está honrando a tu padre, enviando consoladores? ¿No está claro que estos hombres solo han venido para recorrer la tierra y hacer una observación secreta de ella para que puedan vencerla?
sai manyan Ammonawa suka ce wa Hanun, “Kana tsammani Dawuda yana girmama mahaifinka ne da ya aika mutanen nan wurinka su ta’azantar da kai? Ba mutanensa sun zo ne su bincika su kuma leƙi ƙasar su tumɓuke ta ba?”
4 Entonces, Hanun tomó a los sirvientes de David, y cortándose el pelo y las faldas de sus ropas hasta las caderas, dejándolas al descubierto, después los despidió.
Saboda haka Hanun ya kama mutanen Dawuda, ya yi musu aski, ya yayyanka rigunansu a daidai ɗuwawunsu, sa’an nan ya sallame su.
5 Entonces ciertos hombres fueron y le dieron a David la noticia de lo que les habían hecho. Y él envió con el propósito de encontrarlos; porque los hombres fueron grandemente avergonzados. Y el rey dijo: Mantente en Jericó hasta que tu cabello vuelva a ser largo, y luego vuelve.
Da wani ya zo ya faɗa wa Dawuda game da mutanen, sai ya aiki’yan aika su sadu da su, gama an ƙasƙantar da su ainun. Sarki ya ce, “Ku zauna a Yeriko har sai gemunku sun yi girma, sa’an nan ku dawo.”
6 Y cuando los hijos de Amón vieron que se habían hecho odiosos a David, Hanun y los hijos de Amón enviaron mil talentos de plata como pago por los carros de combate y tropas de caballería de Mesopotamia, Siria, Maaca y Soba.
Sa’ad da Ammonawa suka gane cewa sun zama abin wurin a kafan hancin Dawuda, Hanun da Ammonawa suka aika da talenti dubu na azurfa don su yi haya da kekunan yaƙi da mahayan kekunan yaƙi daga Aram-Naharayim, Aram Ma’aka da Zoba.
7 Así que con este dinero tomaron a sueldo treinta y dos mil carros de guerra, y la ayuda del rey de Maaca y su gente, quienes vinieron y tomaron su posición frente a Medeba. Y los hijos de Amón se juntaron de sus pueblos para pelear.
Suka yi hayar kekunan yaƙi da mahayan kekunan yaƙi dubu talatin da biyu, da kuma sarkin Ma’aka tare da mayaƙansa, waɗanda suka zo suka kafa sansani kusa da Medeba, yayinda Ammonawa suka tattaru daga garuruwansu suka fita yaƙi.
8 Y al oírlo David, envió a Joab con todo el ejército de combatientes.
Da jin haka, Dawuda ya aiki Yowab tare da dukan mayaƙa masu yaƙi.
9 Entonces los hijos de Amón salieron y pusieron sus fuerzas en posición en el camino hacia la ciudad; y los reyes que habían venido estaban estacionados solos en el campo.
Ammonawa suka fito suka ja dāgā a ƙofar birninsu, yayinda sarakunan da suka zo, su kansu suka ware suna a fili.
10 Cuando Joab vio que sus fuerzas estaban en posición contra él delante y detrás de él, tomó a los mejores hombres de Israel y los puso en fila contra los arameos;
Yowab ya ga cewa akwai dāgā a gabansa da bayansa; sai ya zaɓi waɗansu mayaƙa mafi kyau a Isra’ila ya sa su a kan Arameyawa.
11 Y el resto de la gente se puso en posición contra los hijos de Amón con Abisai, su hermano, a la cabeza.
Ya sa sauran mutanen a ƙarƙashin kulawar Abishai ɗan’uwansa, aka sa a kan Ammonawa.
12 Y él dijo: Si los arameos son más fuertes y me superan, vengan en mi ayuda; y si los hijos de Amón te superan, acudiré en tu ayuda.
Yowab ya ce, “In Arameyawa suka fi ni ƙarfi, sai ka kawo mini ɗauke da ni; amma in Ammonawa sun fi ka ƙarfi, sai in kawo maka ɗauke.
13 Anímate y seamos fuertes para nuestro pueblo y para los pueblos de nuestro Dios; y que el Señor haga lo que le parezca bien.
Ka yi ƙarfin hali bari mu yi yaƙi da jaruntaka saboda mutanenmu da biranen Allahnmu. Ubangiji zai yi abin da ya ga ya yi masa kyau.”
14 Entonces Joab y las personas que estaban con él avanzaron en la lucha contra los sirios, y huyeron éstos ante él.
Sai Yowab da ƙungiyoyin mayaƙan da suke tare da shi suka matso don su yi yaƙi da Arameyawa, Arameyawan kuwa suka gudu a gabansa.
15 Y cuando los hijos de Amón vieron la huida de los sirios, ellos mismos huyeron de Abisai, su hermano, y entraron en la ciudad. Entonces Joab volvió a Jerusalén.
Sa’ad da Ammonawa suka ga Arameyawa suna gudu, sai su ma suka guda a gaban ɗan’uwansa Abishai suka shiga cikin birni. Sai Yowab ya koma Urushalima.
16 Y cuando los sirios vieron que Israel los había vencido, enviaron hombres a buscar a los sirios que estaban al otro lado del río, con Sofac, el capitán del ejército de Hadadezer, a la cabeza.
Bayan Arameyawa suka ga cewa Isra’ila sun ci su da yaƙi, sai suka aiki’yan aika suka sa aka kawo Arameyawan da suke hayen Kogi waɗanda Shobak shugaban mayaƙan Hadadezer yake shugabanta.
17 Y se le dio a David una palabra de esto; y reunió a todo Israel, pasó por el Jordán y puso sus fuerzas en posición contra ellos. Y cuando las fuerzas de David estaban en posición contra los sirios, se inició la lucha.
Sa’ad da aka faɗa wa Dawuda wannan, sai tattara dukan Isra’ila ya haye Urdun; ya tafi wurinsu ya kuwa ja dāgā ɗaura da su. Dawuda ya ja dāgārsa don yă sadu da Arameyawa a yaƙi, su kuwa suka yi yaƙi da shi.
18 Y los sirios huyeron delante de Israel; y David puso a la espada a los hombres de siete mil carros de guerra arameos y cuarenta mil hombres de infantería, y mató a Sofac, el capitán del ejército.
Amma Arameyawa suka gudu a gaban Isra’ila, mutanen Dawuda kuwa suka kashe masu hawan keken yaƙinsu dubu bakwai da sojojin ƙasa dubu arba’in. Ya kuma kashe Shobak shugaban mayaƙansu.
19 Y cuando los siervos de Hadad Ezer vieron que fueron vencidos por Israel, hicieron la paz con David y se convirtieron en sus siervos. Y Los sirios no ayudarían más a los hijos de Amón.
Da abokan tarayyar Hadadezer suka ga Isra’ila sun ci su da yaƙi, sai suka nemi salama da Dawuda suka kuma zama bayinsa. Saboda haka Arameyawa ba su ƙara yarda su taimaki Ammonawa ba.