< 1 Crónicas 10 >

1 Los filisteos peleaban contra Israel; y los hombres de Israel huyeron ante los filisteos, cayendo heridos en el monte Gilboa.
To, fa, Filistiyawa suka yi yaƙi da Isra’ilawa; Isra’ilawa kuwa suka gudu a gabansu, da yawa kuma suka mutu a kan Dutsen Gilbowa.
2 Y los filisteos siguieron muy de cerca a Saúl y sus hijos, y mataron a Jonatán, Abinadab, Malquisua, los hijos de Saúl.
Filistiyawa suka matsa sosai suna bin Shawulu da’ya’yansa maza, suka kuma kashe’ya’yansa maza Yonatan, Abinadab da Malki-Shuwa.
3 Y la lucha iba contra Saúl, y los arqueros se cruzaron con él, y fue herido por los arqueros.
Yaƙin ya yi tsanani kewaye da Shawulu, kuma sa’ad da maharba suka rutsa shi, sai suka ji masa rauni.
4 Entonces Saúl dijo a su escudero de armas: Toma tu espada y pásala a través de mí, antes de que estos hombres sin circuncisión vengan y se burlen de mí. Pero su sirviente, lleno de miedo, no lo haría. Entonces Saúl sacó su espada, cayó sobre ella.
Sai Shawulu ya ce wa mai riƙe masa kayan yaƙi, “Zare takobinka ka soke ni, in ba haka ba waɗannan marasa kaciya za su zo su yi mini ba’a.” Amma mai ɗaukar masa kayan yaƙi ya ji tsoro bai kuwa yi haka ba; saboda haka Shawulu ya zāre takobinsa ya fāɗi a kansa.
5 Y cuando su siervo vio que Saúl estaba muerto, hizo lo mismo, y murió.
Da mai ɗaukar masa kayan yaƙi ya ga Shawulu ya mutu, sai shi ma ya fāɗi a kan takobinsa ya mutu.
6 Entonces la muerte alcanzó a Saúl y sus tres hijos; Toda su familia llegó a su fin juntos.
Ta haka Shawulu da’ya’yansa maza uku suka mutu, dukan gidansa kuwa suka mutu tare.
7 Y cuando todos los hombres de Israel que estaban en el valle vieron que los hombres de Israel habían huido y que Saúl y sus hijos habían muerto, salieron huyendo de sus pueblos; Y vinieron los filisteos y los tomaron para sí mismos y habitaron allí.
Sa’ad da dukan Isra’ilawa a cikin kwari suka ga cewa mayaƙansu suna gudu, kuma cewa Shawulu da’ya’yansa maza sun mutu, sai suka bar garuruwansu suka gudu. Filistiyawa kuwa suka zo suka zauna a cikinsu.
8 Al día siguiente, cuando los filisteos vinieron a sacar sus bienes de los muertos, vieron a Saúl y sus hijos muertos en el monte Gilboa.
Kashegari, da Filistiyawa suka zo don su tuttuɓe waɗanda suka mutu, sai suka sami Shawulu da’ya’yansa maza sun mutu a Dutsen Gilbowa.
9 Y se lo quitaron todo, y tomaron su cabeza y sus ropas de guerra, y enviaron un mensaje a la tierra de los filisteos para darles la noticia a sus dioses y al pueblo.
Suka tuttuɓe shi suka yanke kansa suka ɗauka duk da kayan yaƙinsa, suka kuma aika’yan aika ko’ina a ƙasar Filistiyawa, a yi shela labarin a cikin gumakansu da kuma mutanensu.
10 Y pusieron sus ropas de guerra en la casa de sus dioses, y pusieron su cabeza en el templo de Dagón.
Suka sa kayan yaƙinsa a haikalin allahnsu suka kuma rataye kansa a haikalin Dagon.
11 Y cuando llegaron las noticias a Jabes de Gala, de lo que los filisteos le habían hecho a Saúl,
Sa’ad da mazaunan Yabesh Gileyad suka ji dukan abin da Filistiyawa suka yi wa Shawulu,
12 Todos los combatientes se acercaron y se llevaron el cuerpo de Saúl y los cuerpos de sus hijos, y los llevaron a Jabes, y enterraron sus huesos debajo del roble en Jabes, y estuvieron en ayuno por siete días.
sai dukan jarumawa suka tafi suka ɗauki jikunan Shawulu da na’ya’yansa maza suka kawo Yabesh. Sa’an nan suka binne ƙasusuwan a ƙarƙashin babban itace oak a Yabesh, suka kuma yi azumi kwana bakwai.
13 Entonces vino a Saúl la muerte por el pecado que hizo contra el Señor, es decir, por la palabra del Señor que no guardó; y porque fue en dirección de una adivina,
Shawulu ya mutu domin rashin aminci ga Ubangiji; bai kiyaye maganar Ubangiji ba, ya ma nemi shawarar mace mai duba,
14 Y no al Señor, por esta razón, lo mató y le dio el reino a David, el hijo de Isaí.
bai kuwa nemi nufin Ubangiji ba. Saboda haka Ubangiji ya kashe shi, ya miƙa mulkin ga Dawuda ɗan Yesse.

< 1 Crónicas 10 >