< Salmos 132 >

1 Canción de las gradas. Acuérdate, oh SEÑOR, de David, de toda su aflicción;
Waƙar haurawa. Ya Ubangiji, ka tuna da Dawuda da kuma dukan irin wuyan da ya jimre.
2 de cómo juró al SEÑOR, prometió al Fuerte de Jacob:
Ya yi rantsuwa ga Ubangiji ya kuma yi alkawari ga Maɗaukaki na Yaƙub cewa,
3 No entraré en la morada de mi casa, ni subiré sobre el lecho de mi estrado;
“Ba zan shiga gidana ko in kwanta a gado ba,
4 no daré sueño a mis ojos, ni a mis párpados adormecimiento,
ba zan ba wa idanuna barci ba, ba gyangyaɗi wa idanuna,
5 hasta que halle lugar para el SEÑOR, moradas para el Fuerte de Jacob.
sai na sami wuri wa Ubangiji, mazauni domin Maɗaukaki na Yaƙub.”
6 He aquí, en Efrata oímos de ella; la hallamos en los campos del bosque.
Mun ji haka a Efrata, muka yi ƙaro da shi a filayen Ya’ar,
7 Entraremos en sus tiendas; adoremos al estrado de sus pies.
“Bari mu tafi wurin zamansa; bari mu yi sujada a wurin sa ƙafafunsa,
8 Levántate, oh SEÑOR, a tu reposo; tú y el arca de tu fortaleza.
ka tashi, ya Ubangiji, ka kuma zo wurin hutunka, kai da akwatin alkawarin ƙarfinka.
9 Tus sacerdotes se vistan de justicia, y se regocijen tus misericordiosos.
Bari a suturta firistocinka da adalci; bari tsarkakanka su rera don farin ciki.”
10 Por amor de David tu siervo no vuelvas de tu ungido el rostro.
Saboda Dawuda bawanka, kada ka ƙi shafaffenka.
11 Juró el SEÑOR verdad a David, no se apartará de ella; del fruto de tu vientre pondré sobre tu trono.
Ubangiji ya rantse wa Dawuda tabbataccen rantsuwa cewa ba zai janye ba cewa, “Ɗaya daga cikin zuriyarka zan sa a kan kursiyinka,
12 Si tus hijos guardaren mi alianza, y mi testimonio que yo les enseñaré; sus hijos también se sentarán sobre tu trono para siempre.
in’ya’yanka maza za su kiyaye alkawari da farillan da na koya musu, to’ya’yansu maza za su zauna a kan kursiyinka har abada abadin.”
13 Porque el SEÑOR ha elegido a Sion; la deseó por habitación para sí.
Gama Ubangiji ya zaɓi Sihiyona, ya so ta zama mazauninsa,
14 Este será mi reposo para siempre; aquí habitaré, porque la he deseado.
“Wannan shi ne wurin hutuna har abada abadin; a nan zan zauna ina mulki gama ina son ta,
15 Bendeciré abundantemente su provisión; a sus pobres saciaré de pan.
zan albarkace ta da tanade-tanade masu yawa; matalautanta za su ƙoshi da abinci.
16 Y a sus sacerdotes vestiré de salud, y sus misericordiosos exultarán de gozo.
Zan suturta firistocinta da ceto, tsarkakanta kuma kullum za su rera don farin ciki.
17 Allí haré reverdecer el cuerno de David; yo he aparejado lámpara a mi ungido.
“A nan zan sa ƙaho ya yi girma wa Dawuda in kuma kafa fitila saboda shafaffena.
18 A sus enemigos vestiré de confusión; y sobre él florecerá su corona.
Zan suturta abokan gābansa da kunya, amma rawanin da yake a kansa zai yi ta walƙiya.”

< Salmos 132 >