< Salmos 118 >

1 Alabad al SEÑOR, porque es bueno; porque para siempre es su misericordia.
Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 Diga ahora Israel: Que para siempre es su misericordia.
Bari Isra’ila yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
3 Diga ahora la casa de Aarón: Que para siempre es su misericordia.
Bari gidan Haruna yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
4 Digan ahora los que temen al SEÑOR: Que eterna es su misericordia.
Bari waɗanda suke tsoron Ubangiji su ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
5 Desde la angustia invoqué a JAH; y me respondió JAH, poniéndome en anchura.
Cikin azabata na yi kuka ga Ubangiji, ya kuwa amsa ta wurin’yantar da ni.
6 El SEÑOR está por mí; no temeré lo que me pueda hacer el hombre.
Ubangiji yana tare da ni; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai yi mini?
7 El SEÑOR está por mí entre los que me ayudan; por tanto yo veré mi deseo en los que me aborrecen.
Ubangiji yana tare da ni; shi ne mai taimakona. Zan yi nasara a kan abokan gābana.
8 Mejor es esperar en el SEÑOR que esperar en hombre.
Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga mutum.
9 Mejor es esperar en el SEÑOR que esperar en príncipes.
Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga sarakuna.
10 Todas las naciones me cercaron; en el nombre del SEÑOR, que yo los talaré.
Dukan al’ummai sun kewaye ni, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
11 Me cercaron y me asediaron; en el nombre del SEÑOR, que yo los talaré.
Sun kewaye ni a kowane gefe, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
12 Me cercaron como abejas, fueron apagados como fuegos de espinos; en el nombre del SEÑOR, que yo los talaré.
Sun rufe ni kamar ƙudan zuma, amma suka mutu nan da nan kamar ƙayayyuwa masu cin wuta; a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
13 Me empujaste con violencia para que cayese; pero el SEÑOR me ayudó.
An ture ni baya na kusa fāɗuwa, amma Ubangiji ya taimake ni.
14 Mi fortaleza y mi canción es JAH, y él me ha sido por salud.
Ubangiji ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.
15 Voz de júbilo y de salud hay en las tiendas de los justos, la diestra del SEÑOR hace valentías.
Sowa ta farin ciki da nasara sun fito a cikin tentunan adalai, “Hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!
16 La diestra del SEÑOR es sublime, la diestra del SEÑOR hace valentías.
An ɗaga hannun dama na Ubangiji sama; hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!”
17 No moriré, sino que viviré, y contaré las obras de JAH.
Ba zan mutu ba amma zan rayu, zan kuwa yi shelar abin da Ubangiji ya yi.
18 Me castigó gravemente JAH, mas no me entregó a la muerte.
Ubangiji ya hore ni sosai, amma bai ba da ni ga mutuwa ba.
19 Abridme las puertas de la justicia, entraré por ellas, alabaré a JAH.
Buɗe mini ƙofofin adalci; zan shiga in kuma yi godiya ga Ubangiji.
20 Esta puerta es del SEÑOR, por ella entrarán los justos.
Wannan ne ƙofar Ubangiji inda adalai za su shiga.
21 Te alabaré porque me has oído, y me fuiste por salud.
Zan yi maka godiya, domin ka amsa mini; ka zama mai cetona.
22 La piedra que desecharon los edificadores, ha venido a ser cabeza del ángulo.
Zabura Dutsen da magina suka ƙi ya zama mai amfani;
23 De parte del SEÑOR es esto, es maravilla en nuestros ojos.
Ubangiji ne ya yi haka, kuma abu mai daraja ne a idanunmu.
24 Este es el día que hizo el SEÑOR, nos gozaremos y alegraremos en él.
Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya yi; bari mu yi farin ciki mu kuma yi murna a cikinta.
25 Oh SEÑOR, salva ahora, te ruego; oh SEÑOR, te ruego nos hagas prosperar ahora.
Ya Ubangiji, ka cece mu; Ya Ubangiji, ka ba mu nasara.
26 Bendito el que viene en Nombre del SEÑOR, desde la Casa del SEÑOR os bendecimos.
Mai albarka ne shi mai zuwa cikin sunan Ubangiji. Daga gidan Ubangiji muna sa muku albarka.
27 Dios es el SEÑOR que nos ha resplandecido, atad el sacrificio con cuerdas a los cuernos del altar.
Ubangiji shi ne Allah ya kuma sa haskensa ya haskaka a kanmu. Da kwanoni a hannunmu, muka shiga jerin gwanon biki ku kai su ƙahoni na bagade.
28 Mi Dios eres tú, y a ti alabaré; Dios mío, a ti ensalzaré.
Kai ne Allahna, zan kuwa yi maka godiya; kai ne Allahna, zan kuwa ɗaukaka ka.
29 Alabad al SEÑOR, porque es bueno; porque para siempre es su misericordia.
Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.

< Salmos 118 >