< Salmos 109 >

1 Al Vencedor: de David: Salmo. Oh Dios de mi alabanza, no calles;
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Allah, wanda nake yabo, kada ka yi shiru,
2 porque boca de impío y boca de engañador se han abierto sobre mí; han hablado de mí con lengua mentirosa,
gama mugaye da masu ruɗu sun buɗe bakunansu a kaina; sun yi magana a kaina da harsunan ƙarya.
3 y con palabras de odio me rodearon; y pelearon contra mí sin causa.
Da kalmomin ƙiyayya sun kewaye ni; sun tasar mini ba dalili.
4 En pago de mi amor me han sido adversarios; mas yo oraba.
A maimakon ƙauna sun sāka mini da zargi, amma ni mutum ne mai addu’a.
5 Y pusieron contra mí mal por bien, y odio por mi amor.
Sun sāka mini alheri da mugunta, ƙauna kuma da ƙiyayya.
6 Pon sobre él al impío; y Satanás esté a su diestra.
Ka naɗa mugun mutum yă yi hamayya da shi; bari mai zargi yă tsaya a hannun damansa.
7 Cuando fuere juzgado, salga impío; y su oración sea para pecado.
Sa’ad da aka yi masa shari’a, bari a same shi da laifi, bari kuma addu’o’insa su hukunta shi.
8 Sean sus días pocos; tome otro su oficio.
Bari kwanakinsa su zama kaɗan; bari wani yă ɗauki wurinsa na shugabanci.
9 Sean sus hijos huérfanos, y su mujer viuda.
Bari’ya’yansa su zama marayu matarsa kuma gwauruwa.
10 Y anden sus hijos vagabundos, y mendiguen; y procuren de sus desiertos.
Bari’ya’yansa su zama masu yawo suna bara; bari a yi ta koransu daga gidajensu da suke kufai.
11 Enrede el acreedor todo lo que tiene, y extraños saqueen su trabajo.
Bari mai binsa bashi yă ƙwace dukan abin da yake da shi; bari baƙi su washe amfanin aikinsa.
12 No tenga quien le haga misericordia; ni haya quien tenga compasión de sus huérfanos.
Bari kada kowa yă yi masa alheri ko yă ji tausayin marayunsa.
13 Su posteridad sea talada; en segunda generación sea raído su nombre.
Bari duk zuriyarsa su mutu, a shafe sunayensu daga tsara mai zuwa.
14 Venga en memoria cerca del SEÑOR la maldad de sus padres, y el pecado de su madre no sea borrado.
Bari a tuna da laifin kakanninsa a gaban Ubangiji; bari kada a taɓa shafe zunubin mahaifiyarsa.
15 Estén siempre delante del SEÑOR, y él corte de la tierra su memoria.
Bari zunubansu su kasance a gaban Ubangiji kullum, don yă sa a manta da su daga duniya.
16 Por cuanto no se acordó de hacer misericordia, y persiguió al varón pobre en espíritu, y menesteroso, y quebrantado de corazón, para matarlo.
Gama bai taɓa yin tunanin yin alheri ba, amma ya tsananta wa matalauta da mabukata da kuma masu fid da zuciya har suka mutu.
17 Y amó la maldición, y ésta le sobrevino; y no quiso la bendición, y ella se alejó de él.
Yana jin daɗin la’antarwa, bari yă dawo a kansa; ba ya son sa albarka, bari kada kowa yă sa masa albarka.
18 Y se vistió de maldición como de su vestido, y entró como agua en sus entrañas, y como aceite en sus huesos.
Ya sa la’antarwa kamar rigarsa; ta shiga cikin jikinsa kamar ruwa, cikin ƙasusuwansa kamar mai.
19 Séale como vestido con que se cubra, y en lugar del cinto con que se ciña siempre.
Bari tă zama kamar mayafin da aka ɗaura kewaye da shi, kamar ɗamara da aka ɗaura kewaye da shi har abada.
20 Este sea el pago de parte del SEÑOR de los que me calumnian, y de los que hablan mal contra mi alma.
Bari wannan yă zama sakayyar Ubangiji ga masu zargina, ga waɗanda suke mugayen maganganu a kaina.
21 Y tú, oh DIOS el Señor, haz conmigo por amor de tu Nombre: Líbrame, porque tu misericordia es buena.
Amma kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi da ni da kyau saboda sunanka; ta alherin ƙaunarka, ka cece ni.
22 Porque yo soy pobre y necesitado; y mi corazón está herido dentro de mí.
Gama ni matalauci ne mai bukata kuma, zuciyata kuwa ta yi rauni a cikina.
23 Como la sombra cuando declina me voy; soy arrebatado del viento como langosta.
Na ɓace kamar inuwar yamma; ana kakkaɓe ni kamar fāra.
24 Mis rodillas están debilitadas a causa del ayuno, y mi carne desfallecida por falta de gordura.
Gwiwoyina suna mutuwa saboda azumi; jikina ya rame ba kuma ƙarfi.
25 Yo he sido para ellos objeto de oprobio; me miraban, y meneaban su cabeza.
Na zama abin dariya ga masu zargina; sa’ad da suka gan ni, suka kaɗa kawunansu.
26 Ayúdame, SEÑOR Dios mío; sálvame conforme a tu misericordia.
Ka taimake ni, ya Ubangiji Allahna; ka cece ni bisa ga ƙaunarka.
27 Y entiendan que esta es tu mano; que tú, el SEÑOR, has hecho esto.
Bari su san cewa hannunka ne, cewa kai ne, ya Ubangiji, ka yi shi.
28 Maldigan ellos, y bendice tú; levántense, mas sean avergonzados; y tu siervo sea alegrado.
Za su iya la’anta, amma kai za ka sa albarka; sa’ad da suka tasar za su sha kunya, amma bawanka zai yi farin ciki.
29 Sean vestidos de vergüenza los que me calumnian; y sean cubiertos de su confusión como con un manto.
Masu zargina za su sha kunya za a rufe su da kunya kamar mayafi.
30 Yo alabaré al SEÑOR en gran manera con mi boca, y le loaré en medio de muchos.
Da bakina zan ɗaukaka Ubangiji sosai; cikin babban taro zan yabe shi.
31 Porque él se pondrá a la diestra del pobre en espíritu, para librar su alma de los que le juzgan.
Gama yana tsaya a hannun damar mai bukata, don yă cece ransa daga waɗanda suke hukunta shi.

< Salmos 109 >