< Salmos 107 >

1 Alabad al SEÑOR, porque es bueno; porque para siempre es su misericordia.
Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 Diganlo los redimidos del SEÑOR, los que ha redimido del poder del enemigo,
Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
3 y los ha congregado de las tierras, del oriente y del occidente, del aquilón y del mar.
su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
4 Anduvieron perdidos por el desierto, por la soledad sin camino, sin hallar ciudad en dónde vivir.
Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
5 Hambrientos y sedientos, su alma desfallecía en ellos.
Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
6 Y clamaron al SEÑOR en su angustia, los libró de sus aflicciones.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
7 Los dirigió por camino derecho, para que viniesen a ciudad de habitación.
Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
8 Alaben al SEÑOR por su misericordia; y sus maravillas para con los hijos de los hombres.
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
9 Porque sació al alma menesterosa, y llenó de bien al alma hambrienta.
gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
10 Los que moraban en tinieblas y sombra de muerte aprisionados, en aflicción y en hierros,
Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
11 por cuanto fueron rebeldes a las palabras del SEÑOR, y aborrecieron el consejo del Altísimo.
gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
12 Por eso quebrantó él con trabajo sus corazones, cayeron y no hubo quién los ayudase.
Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
13 Luego que clamaron al SEÑOR en su angustia, los libró de sus aflicciones.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
14 Los sacó de las tinieblas, y de la sombra de muerte; y rompió sus prisiones.
Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
15 Alaben al SEÑOR por su misericordia, y sus maravillas para con los hijos de los hombres.
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
16 Porque quebrantó las puertas de bronce, y desmenuzó los cerrojos de hierro.
gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
17 Los locos, a causa del camino de su rebelión; y a causa de sus maldades fueron afligidos,
Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
18 su alma abominó toda vianda; y llegaron hasta las puertas de la muerte.
Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
19 Mas clamaron al SEÑOR en su angustia; y los salvó de sus aflicciones.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
20 Envió su palabra, y los curó, y los libró de sus sepulturas.
Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
21 Alaben al SEÑOR por su misericordia, y sus maravillas para con los hijos de los hombres.
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
22 Y ofrezcan sacrificios de alabanza, y publiquen sus obras con júbilo.
Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
23 Los que descienden al mar en navíos, y hacen obra en las muchas aguas,
Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
24 ellos han visto las obras del SEÑOR, y sus maravillas en el mar profundo.
Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
25 El dijo, e hizo saltar el viento de la tempestad, que levanta sus ondas;
Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
26 suben a los cielos, descienden a los abismos; sus almas se derriten con el mal.
Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
27 Tiemblan, y titubean como borrachos, y toda su ciencia es perdida;
Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
28 claman al SEÑOR en su angustia, y los libra de sus aflicciones.
Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
29 Hace parar la tempestad en sosiego, y sus ondas cesan.
Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
30 Se alegran luego porque se reposaron; y él los guía al término de su voluntad.
Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
31 Alaben al SEÑOR por su misericordia, y sus maravillas para con los hijos de los hombres.
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
32 Y ensálcenlo en la congregación del pueblo; y en la reunión de ancianos lo alaben.
Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
33 El puso los ríos en desierto, y los manaderos de las aguas en sed;
Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
34 la tierra fructífera en salados; por la maldad de los que la habitan.
ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
35 Vuelve el desierto en estanques de aguas, y la tierra desierta en manaderos de agua.
Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
36 Y aposenta allí hambrientos, y aderezan allí ciudad para habitación;
a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
37 y siembran campos, y plantan viñas; y rinden fruto de aumento.
Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
38 Y los bendice, y se multiplican en gran manera; y no disminuye sus bestias.
ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
39 Y después son menoscabados, y abatidos de tiranía; de males y congojas.
Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
40 El derrama menosprecio sobre los príncipes, y les hace andar errados, vagabundos, sin camino.
shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
41 Y levanta al pobre de la pobreza, y vuelve las familias como ovejas.
Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
42 Vean los rectos, y alégrense; y toda maldad cierre su boca.
Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
43 ¿Quién es sabio y guardará estas cosas, y entenderá las misericordias del SEÑOR?
Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.

< Salmos 107 >