< Job 29 >
1 Y volvió Job a tomar su propósito, y dijo:
Ayuba ya ci gaba da jawabinsa,
2 ¡Quién me volviese como en los meses pasados, como en los días cuando Dios me guardaba,
“Da ma ina nan lokacin da ya wuce baya can, kwanakin da Allah yake lura da ni,
3 cuando hacía resplandecer su candela sobre mi cabeza, a la luz de la cual yo caminaba en la oscuridad;
lokacin da fitilarsa take haske a kaina na yi tafiya cikin duhu tare da haskensa.
4 como fue en los días de mi juventud, cuando Dios era familiar en mi tienda;
Kwanakin da nake tasowa, lokacin da abokantakar Allah ta sa wa gidana albarka,
5 cuando aún el Omnipotente estaba conmigo, y mis hijos alrededor de mí;
lokacin da Maɗaukaki yana tare da ni, kuma’ya’yana suna kewaye da ni,
6 cuando lavaba yo mis caminos con manteca, y la piedra me derramaba ríos de aceite!
lokacin da ake zuba madara a inda nake takawa, duwatsu kuma suna ɓulɓulo mini man zaitun.
7 Cuando salía a la puerta a juicio, y en la plaza hacía aparejar mi silla,
“Sa’ad da na je ƙofar birni na zauna a bainin jama’a,
8 Los jóvenes me veían, y se escondían; y los viejos se levantaban, y estaban en pie.
matasan da suka gan ni sukan ja gefe tsofaffi kuma suka tashi tsaye;
9 Los príncipes detenían sus palabras; ponían la mano sobre su boca;
sarakuna suka yi shiru suka rufe bakunansu da hannuwansu;
10 la voz de los principales se ocultaba, y su lengua se pegaba a su paladar;
Muryar manya ta yi tsit harshensu ya manne a rufin bakunansu.
11 cuando los oídos que me oían, me llamaban bienaventurado, y los ojos que me veían, me daban testimonio.
Duk wanda ya ji ni ya yaba mini waɗanda suka gan ni kuma sun amince da ni,
12 Porque libraba al pobre que gritaba, y al huérfano que carecía de ayudador.
domin na ceci matalauta waɗanda suka nemi taimako, da marasa mahaifi waɗanda ba su da wanda zai taimake su.
13 La bendición del que se iba a perder venía sobre mí; y al corazón de la viuda daba alegría.
Mutumin da yake bakin mutuwa ya sa mini albarka. Na faranta wa gwauruwa zuciya.
14 Me vestía de justicia, y ella me cubría como un manto; y mi diadema era juicio.
Na yafa adalci ya zama suturata; gaskiya ita ce rigata da rawanina.
15 Yo era ojos al ciego, y pies al cojo.
Ni ne idon makafi kuma ƙafa ga guragu.
16 A los menesterosos era padre; y de la causa que no entendía, me informaba con diligencia.
Ni mahaifi ne ga masu bukata; na tsaya wa baƙo.
17 Y quebraba los colmillos del inicuo, y de sus dientes hacía soltar la presa.
Na karya ƙarfin mugaye na ƙwato waɗanda suke riƙe da haƙoransu.
18 Y decía yo: En mi nido moriré, y como arena multiplicaré días.
“Na yi tunani cewa, ‘Zan mutu a cikin gidana, kwanakina da yawa kamar turɓayar ƙasa.
19 Mi raíz está abierta junto a las aguas, y en mis ramas permanecerá rocío.
Jijiyoyina za su kai cikin ruwa, kuma raɓa za tă kwanta a rassana dukan dare.
20 Mi honra se renueva conmigo, y mi arco se renueva en mi mano.
Ɗaukakata za tă kasance tare da ni garau, bakana koyaushe sabo ne a hannuna.’
21 Me oían, y esperaban; y callaban a mi consejo.
“Mutane suna mai da hankali su saurare ni, suna yin shiru don su ji shawarata.
22 Tras mi palabra no replicaban, mas mi razón destilaba sobre ellos.
Bayan da na yi magana, ba su ƙara ce kome ba. Maganata ta shige su.
23 Me esperaban como a la lluvia, y abrían su boca como a la lluvia tardía.
Sukan jira ni kamar yadda ake jiran ruwan sama. Sukan sha daga cikin maganganuna kamar mai shan ruwan bazara.
24 Si me reía a ellos, no lo creían; y no abatían la luz de mi rostro.
Sa’ad da na yi musu murmushi da ƙyar sukan yarda; hasken fuskata yana da daraja a gare su.
25 Aprobaba el camino de ellos, y me sentaba en cabecera; y moraba como rey en el ejército, como el que consuela llorosos.
Na zaɓar masu inda za su bi na kuma zauna kamar sarkinsu; na zauna kamar sarki a cikin rundunansu; ina nan kamar mai yi wa masu makoki ta’aziyya.