< Job 27 >
1 Y volvió Job a tomar su propósito, y dijo:
Ayuba kuwa ya ci gaba da magana,
2 Vive el Dios que me quitó mi derecho, y el Omnipotente, que amargó mi alma,
“Na rantse da Allah mai rai, wanda ya danne mini gaskiyata, Maɗaukaki, wanda ya sa nake cikin ɗacin rai.
3 que todo el tiempo que mi alma estuviere en mí, y hubiere hálito de Dios en mis narices,
Muddin ina da rai a cikina kuma numfashin Allah yana cikin hancina,
4 mis labios no hablarán iniquidad, ni mi lengua pronunciará engaño.
bakina ba zai faɗi mugun abu ba, harshena kuma ba zai yi ƙarya ba.
5 Nunca tal me acontezca que yo os justifique; hasta morir no quitaré de mí mi integridad.
Ba zan taɓa yarda cewa kuna da gaskiya ba; har in mutu, ba zan daina kāre mutuncina ba.
6 Mi justicia tengo asida, y no la cederé; no me reprochará mi corazón en todos mis días.
Zan ci gaba da adalcina, ba zan fasa ba; lamirina ba zai taɓa yashe ni ba, dukan kwanakin raina.
7 Sea como el impío mi enemigo, y como el inicuo mi adversario.
“Bari maƙiyana su zama kamar mugaye, masu gāba da ni kuma su zama kamar marasa adalci.
8 Porque ¿cuál es la esperanza del hipócrita, por mucho que hubiere robado, cuando Dios arrebatare su alma?
Gama wane bege marar tsoron Allah yake da shi, lokacin da aka datse shi, lokacin da Allah ya ɗauke ransa?
9 ¿Por ventura oirá Dios su clamor cuando la tribulación viniere sobre él?
Ko Allah yana sauraron kukansa lokacin da ƙunci ya auko masa?
10 ¿Por ventura se deleitará en el Omnipotente? ¿Invocará a Dios en todo tiempo?
Ko zai sami farin ciki daga Maɗaukaki? Ko zai yi kira ga Allah a kowane lokaci?
11 Yo os enseñaré lo que hay en la mano de Dios; no esconderé lo que hay acerca del Omnipotente.
“Zan koya muku game da ikon Allah; ba zan ɓoye hanyoyin Maɗaukaki ba.
12 He aquí que todos vosotros lo habéis visto, ¿por qué pues os desvanecéis con vanidad?
Duk kun ga wannan ku da kanku saboda haka me ya sa kuke maganganun nan marasa ma’ana?
13 Esta es para con Dios la suerte del hombre impío, y la herencia que los violentos han de recibir del Omnipotente.
“Ga abin da mugaye za su samu gādon da azzalumi zai samu daga Maɗaukaki.
14 Si sus hijos fueren multiplicados, serán para el cuchillo; y sus pequeños no se saciarán de pan.
Kome yawan’ya’yansa, takobi za tă gama da su; zuriyarsa ba za su taɓa samun isashen abinci ba.
15 Los que de ellos quedaren, en muerte serán sepultados; y no llorarán sus viudas.
Waɗanda suka tsira annoba za tă kashe su, kuma gwaurayensu ba za su yi kukan mutuwarsu ba.
16 Si amontonare plata como polvo, y si preparare ropa como lodo;
Ko da yake ya tara azurfa kamar ƙasa, tufafi kuma kamar tarin ƙasa,
17 la habrá preparado él, mas el justo se vestirá, y el inocente repartirá la plata.
abin da ya tara masu adalci za su sa marasa laifi za su raba azurfarsa.
18 Edificó su casa como la polilla, y como cabaña que el guarda hizo.
Gidan da ya gina kamar gidan gizo-gizo, kamar bukkar mai tsaro.
19 El rico dormirá, mas no será recogido; abrirá sus ojos, y no verá a nadie.
Attajiri zai kwanta, amma daga wannan shi ke nan; lokacin da zai buɗe idanunsa, kome ya tafi.
20 Asirán de él terrores como aguas; torbellino lo arrebatará de noche.
Tsoro zai kwashe shi kamar ambaliyar ruwa; Da dare iska za tă tafi da shi.
21 Lo tomará el solano, y partirá; y tempestad lo arrebatará del lugar suyo.
Iskar gabas za tă tafi da shi; shi ke nan ya ƙare; za tă share shi daga wurinsa.
22 Dios, pues, descargará sobre él, y no perdonará. Hará él por huir de su mano.
Za tă murɗe shi ba tausayi, lokacin da yake guje wa ikon iskar.
23 Batirán sus manos sobre él, y desde su lugar le silbarán.
Zai tafa hannu yă yi tsaki yă kawar da shi daga wurinsa.”