< Génesis 10 >

1 Estas son las generaciones de los hijos de Noé: Sem, Cam y Jafet, a los cuales nacieron hijos después del diluvio.
Wannan shi ne labarin Shem, Ham da Yafet,’ya’yan Nuhu maza, waɗanda su ma sun haifi’ya’ya maza bayan ambaliyar.
2 Los hijos de Jafet: Gomer, y Magog, y Madai, y Javán, y Tubal, y Mesec, y Tiras.
’Ya’yan Yafet maza su ne, Gomer, Magog, Madai da Yaban, Tubal, Meshek, da kuma Tiras.
3 Y los hijos de Gomer: Askenaz, y Rifat, y Togarma.
’Ya’yan Gomer maza su ne, Ashkenaz, Rifat, da Togarma.
4 Y los hijos de Javán: Elisa, y Tarsis, Quitim, y Dodanim.
’Ya’yan maza Yaban su ne, Elisha, Tarshish, Kittim da Rodanim.
5 Por éstos fueron partidas las islas de los gentiles en sus tierras, cada cual según su lengua, conforme a sus familias en sus naciones.
(Daga waɗannan mutane ne masu zama a bakin teku suka bazu zuwa cikin ƙasashensu da kuma cikin al’ummansu, kowanne da yarensa.)
6 Los hijos de Cam: Cus, y Mizraim, y Fut, y Canaán.
’Ya’yan Ham maza su ne, Kush, Masar, Fut, da Kan’ana.
7 Y los hijos de Cus: Seba, Havila, y Sabta, y Raama, y Sabteca. Y los hijos de Raama: Seba y Dedán.
’Ya’yan Kush maza su ne, Seba, Hawila, Sabta, Ra’ama da Sabteka.’Ya’yan Ra’ama maza kuwa su ne, Sheba da Dedan.
8 Y Cus engendró a Nimrod. Este comenzó a ser poderoso en la tierra.
Kush shi ne mahaifin Nimrod wanda ya yi girma ya zama jarumin yaƙi a duniya.
9 Este fue poderoso cazador delante del SEÑOR; por lo cual se dice: Así como Nimrod poderoso cazador delante del SEÑOR.
Shi babban maharbi ne a gaban Ubangiji. Shi ya sa akan ce, kamar Nimrod babban maharbi a gaban Ubangiji.
10 Y fue la cabecera de su reino Babel, y Erec, y Acad, y Calne, en la tierra de Sinar.
Cibiyoyin mulkinsa na farko su ne Babilon, Erek, Akkad, da Kalne a cikin Shinar.
11 De esta tierra salió Assur, el cual edificó a Nínive, y a Rehobot, y a Cala,
Daga wannan ƙasa, sai ya tafi Assuriya, inda ya gina Ninebe, Rehobot Ir, Kala
12 Y a Resén entre Nínive y Cala; la cual es la ciudad grande.
da Resen, wadda take tsakanin Ninebe da Kala; wanda yake babban birni.
13 Y Mizraim engendró a Ludim, y a Anamim, y a Lehabim, y a Naftuhim,
Mizrayim shi ne mahaifin Ludiyawa, Anamawa, Lehabiyawa, Naftuhiyawa,
14 Y a Patrusim, y a Casluhim de donde salieron los filisteos, y a Caftorim.
Fetrusiyawa, da Kasluhiyawa (inda Filistiyawa suka fito) da kuma Kaftorawa.
15 Y Canaán engendró a Sidón, su primogénito y a Het,
Kan’ana shi ne mahaifin, Sidon ɗan farinsa, da na Hittiyawa,
16 y a Jebusi, y a Amorri, y a Gergesi,
Yebusiyawa, Amoriyawa, Girgashiyawa,
17 y a Hevi, y a Arci, y a Sini,
Hiwiyawa, Arkiyawa, Siniyawa,
18 y a Aradi, y a Samari, y a Amati; y después se derramaron las familias de los cananeos.
Arbadiyawa, Zemarawa, da Hamawa. Daga baya zuriyar Kan’aniyawa suka yaɗu
19 Y fue el término de los cananeos desde Sidón, viniendo a Gerar hasta Gaza, hasta entrar en Sodoma y Gomorra, Adma, y Zeboim hasta Lasa.
har iyakar Kan’ana ta kai Sidon ta wajen Gerar har zuwa Gaza, sa’an nan ta milla zuwa Sodom, Gomorra, Adma da Zeboyim, har zuwa Lasha.
20 Estos son los hijos de Cam por sus familias, por sus lenguas, en sus tierras, en sus naciones.
Waɗannan su ne’ya’yan Ham maza bisa ga zuriyarsu da yarurrukansu, cikin ƙasashensu da kuma al’ummominsu.
21 También le nacieron hijos a Sem, padre de todos los hijos de Heber, y hermano mayor de Jafet.
Aka kuma haifa wa Shem, wan Yafet,’ya’ya maza. Shem shi ne kakan’ya’yan Eber duka.
22 Y los hijos de Sem: Elam, y Asur, y Arfaxad, y Lud, y Aram.
’Ya’yan Shem maza su ne, Elam, Asshur, Arfakshad, Lud da Aram.
23 Y los hijos de Aram: Uz, y Hul, y Geter, y Mas.
’Ya’yan Aram maza su ne, Uz, Hul, Geter da Mash.
24 Y Arfaxad engendró a Sala, y Sala engendró a Heber.
Arfakshad ne mahaifin Shela. Shela kuma shi ne mahaifin Eber.
25 Y a Heber nacieron dos hijos: el nombre del uno fue Peleg, porque en sus días fue partida la tierra; y el nombre de su hermano, Joctán.
Aka haifa wa Eber’ya’ya maza biyu. Aka ba wa ɗaya suna Feleg, gama a zamaninsa ne aka raba duniya; aka kuma sa wa ɗan’uwansa suna Yoktan.
26 Y Joctán engendró a Almodad, y a Selef, y Hazar-mavet, y a Jera,
Yoktan shi ne mahaifin, Almodad, Shelef, Hazarmawet, Yera,
27 y a Adoram, y a Uzal, y a Dicla,
Hadoram, Uzal, Dikla,
28 y a Obal, y a Abimael, y a Seba,
Obal, Abimayel, Sheba,
29 y a Ofir, y a Havila, y a Jobab: todos éstos fueron hijos de Joctán.
Ofir, Hawila da Yobab. Dukan waɗannan’ya’yan Yoktan maza ne.
30 Y fue su habitación desde Mesa viniendo de Sefar, monte de oriente.
Yankin da suka zauna ya miƙe daga Mesha zuwa wajen Sefar a gabashin ƙasar tudu.
31 Estos fueron los hijos de Sem por sus familias, por sus lenguas, en sus tierras, en sus naciones.
Waɗannan su ne’ya’yan Shem maza bisa ga zuriyarsu da yarurrukansu, cikin ƙasashensu da kuma al’ummominsu.
32 Estas son las familias de Noé por su descendencia, en sus naciones; y de éstas, fueron divididos los gentiles en la tierra después del diluvio.
Waɗannan su ne zuriyar’ya’yan Nuhu maza bisa ga jerin zuriyarsu cikin al’ummominsu. Daga waɗannan ne al’ummomi suka bazu ko’ina a duniya bayan ambaliya.

< Génesis 10 >