< Salmos 95 >

1 VENID, celebremos alegremente á Jehová: cantemos con júbilo á la roca de nuestra salud.
Ku zo, bari mu rera don farin ciki ga Ubangiji; bari mu yi sowa da ƙarfi ga Dutsen cetonmu.
2 Lleguemos ante su acatamiento con alabanza; aclamémosle con cánticos.
Bari mu zo gabansa da godiya mu rera gare shi da kiɗi da waƙa.
3 Porque Jehová es Dios grande; y Rey grande sobre todos los dioses.
Gama Ubangiji Allah mai girma ne, babban Sarki a bisa dukan alloli.
4 Porque en su mano están las profundidades de la tierra, y las alturas de los montes son suyas.
A hannunsa ne zurfafan duniya suke, ƙwanƙolin dutse kuma nasa ne.
5 Suya también la mar, pues él la hizo; y sus manos formaron la seca.
Teku nasa ne, gama shi ne ya yi shi, da hannuwansa kuma ya yi busasshiyar ƙasa.
6 Venid, adoremos y postrémonos; arrodillémonos delante de Jehová nuestro hacedor.
Ku zo, bari mu rusuna mu yi sujada, bari mu durƙusa a gaban Ubangiji Mahaliccinmu;
7 Porque él es nuestro Dios; nosotros el pueblo de su dehesa, y ovejas de su mano. Si hoy oyereis su voz,
gama shi ne Allahnmu mu mutanen makiyayansa ne, garke kuwa a ƙarƙashin kulawarsa. Yau, in kuka ji muryarsa,
8 No endurezcáis vuestro corazón como en Meriba, como el día de Masa en el desierto;
“Kada ku taurare zukatanku kamar yadda kuka yi a Meriba, kamar yadda kuka yi a wancan rana a Massa a hamada,
9 Donde me tentaron vuestros padres, probáronme, y vieron mi obra.
inda kakanninku suka gwada suka kuma jarraba ni, ko da yake sun ga abin da na yi.
10 Cuarenta años estuve disgustado con la nación, y dije: Pueblo es que divaga de corazón, y no han conocido mis caminos.
Shekara arba’in na yi fushi da wancan tsara; na ce, ‘Su mutane ne waɗanda zukatansu suka kauce, kuma ba su san hanyoyina ba.’
11 Por tanto juré en mi furor que no entrarían en mi reposo.
Saboda haka na yi rantsuwa cikin fushina, ‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’”

< Salmos 95 >