< Salmos 73 >
1 Salmo de Asaph. CIERTAMENTE bueno es Dios á Israel, á los limpios de corazón.
Zabura ta Asaf. Tabbatacce Allah mai alheri ne ga Isra’ila, ga waɗanda suke masu tsabta a zuciya.
2 Mas yo, casi se deslizaron mis pies; por poco resbalaron mis pasos.
Amma game da ni, ƙafafuna suna gab da yin santsi; tafin ƙafana ya yi kusan zamewa.
3 Porque tuve envidia de los insensatos, viendo la prosperidad de los impíos.
Gama na yi kishin masu girman kai sa’ad da na ga cin gaban da masu mugunta suke yi.
4 Porque no hay ataduras para su muerte; antes su fortaleza está entera.
Ba sa yin wata fama; jikunansu lafiya suke da kuma ƙarfi.
5 No están ellos en el trabajo humano; ni son azotados con [los otros] hombres.
Ba sa shan wata wahalar da sauran mutane ke sha; ba su da damuwa irin na’yan adam.
6 Por tanto soberbia los corona: cúbrense de vestido de violencia.
Saboda girman kai ya zama musu abin wuya; tā da hankali ya zama musu riga.
7 Sus ojos están salidos de gruesos: logran con creces los antojos del corazón.
Daga mugayen zukatansu laifi kan fito mugaye ƙulle-ƙullen da suke cikin zukatansu ba su da iyaka.
8 Soltáronse, y hablan con maldad de [hacer] violencia; hablan con altanería.
Suna ba’a, suna faɗin mugayen abubuwa; cikin girman kan suna barazana yin danniya.
9 Ponen en el cielo su boca, y su lengua pasea la tierra.
Bakunansu na cewa sama na su ne, kuma harsunansu sun mallaki duniya.
10 Por eso su pueblo vuelve aquí, y aguas de lleno les son exprimidas.
Saboda haka mutanensu sun juya gare su suna kuma shan ruwa a yalwace.
11 Y dicen: ¿Cómo sabe Dios? ¿y hay conocimiento en lo alto?
Suna cewa, “Yaya Allah zai sani? Mafi Ɗaukaka yana da sani ne?”
12 He aquí estos impíos, sin ser turbados del mundo, alcanzaron riquezas.
Ga yadda mugaye suke, kullum ba su da damuwa, arzikinsu yana ta ƙaruwa.
13 Verdaderamente en vano he limpiado mi corazón, y lavado mis manos en inocencia;
Tabbatacce a banza na bar zuciyata da tsabta; a banza na wanke hannuwa don nuna rashin laifi.
14 Pues he sido azotado todo el día, [y empezaba] mi castigo por las mañanas.
Dukan yini na sha annoba; an hukunta ni kowace safiya.
15 Si dijera yo, Discurriré de esa suerte; he aquí habría negado la nación de tus hijos:
Da na ce, “Zan faɗa haka,” da na bashe’ya’yanka.
16 Pensaré pues para saber esto: es á mis ojos [duro] trabajo,
Sa’ad da na yi ƙoƙari in gane wannan, sai ya zama danniya a gare ni
17 Hasta que venido al santuario de Dios, entenderé la postrimería de ellos.
sai da na shiga wuri mai tsarki na Allah; sa’an nan na gane abin da ƙarshensu zai zama.
18 Ciertamente los has puesto en deslizaderos; en asolamientos los harás caer.
Tabbatacce ka sa su a ƙasa mai santsi; ka jefar da su ga hallaka.
19 ¡Cómo han sido asolados! ¡cuán en un punto! Acabáronse, fenecieron con turbaciones.
Duba yadda suka hallaka farat ɗaya, razana ta share su gaba ɗaya!
20 Como sueño del que despierta, así, Señor, cuando despertares, menospreciarás sus apariencias.
Kamar yadda mafarki yake sa’ad da mutum ya farka, haka yake sa’ad da ka farka, ya Ubangiji, za ka rena su kamar almarai.
21 Desazonóse á la verdad mi corazón, y en mis riñones sentía punzadas.
Sa’ad da zuciyata ta ɓaci hankalina kuma ya tashi,
22 Mas yo era ignorante, y no entendía: era como una bestia acerca de ti.
na zama marar azanci da jahili; na zama kamar dabba a gabanka.
23 Con todo, yo siempre estuve contigo: trabaste de mi mano derecha.
Duk da haka kullum ina tare da kai; ka riƙe ni a hannun damana.
24 Hasme guiado según tu consejo, y después me recibirás en gloria.
Ka bishe ni da shawararka, bayan haka kuma za ka kai ni cikin ɗaukaka.
25 ¿A quién tengo yo en los cielos? Y fuera de ti nada deseo en la tierra.
Wa nake da shi a sama in ba kai ba? Ba na kuma sha’awar kome a duniya in ban da kai.
26 Mi carne y mi corazón desfallecen: [mas] la roca de mi corazón y mi porción es Dios para siempre.
Jikina da zuciyata za su iya raunana, amma Allah ne ƙarfin zuciyata da kuma rabona har abada.
27 Porque he aquí, los que se alejan de ti perecerán: tú cortarás á todo aquel que fornicando, de ti [se aparta].
Waɗanda suke nesa da kai za su hallaka; kakan hallaka dukan waɗanda suke maka rashin aminci.
28 Y en cuanto á mí, el acercarme á Dios es el bien: he puesto en el Señor Jehová mi esperanza, para contar todas tus obras.
Amma game da ni, yana da kyau in kasance kusa da Allah. Na mai da Ubangiji Mai Iko Duka mafakata; zan yi shelar dukan ayyukanka.