< Salmos 66 >

1 Al Músico principal: Cántico: Salmo. ACLAMAD á Dios con alegría, toda la tierra:
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
2 Cantad la gloria de su nombre: poned gloria [en] su alabanza.
Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
3 Decid á Dios: ¡Cuán terribles tus obras! Por lo grande de tu fortaleza te mentirán tus enemigos.
Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
4 Toda la tierra te adorará, y cantará á ti; cantarán á tu nombre. (Selah)
Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” (Sela)
5 Venid, y ved las obras de Dios, terrible en hechos sobre los hijos de los hombres.
Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
6 Volvió la mar en seco; por el río pasaron á pie; allí en él nos alegramos.
Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
7 El se enseñorea con su fortaleza para siempre: sus ojos atalayan sobre las gentes: los rebeldes no serán ensalzados. (Selah)
Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada’yan tawaye su tayar masa. (Sela)
8 Bendecid, pueblos, á nuestro Dios, y haced oir la voz de su alabanza.
Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
9 El [es el] que puso nuestra alma en vida, y no permitió que nuestros pies resbalasen.
ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
10 Porque tú nos probaste, oh Dios: ensayástenos como se afina la plata.
Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
11 Nos metiste en la red; pusiste apretura en nuestros lomos.
Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
12 Hombres hiciste subir sobre nuestra cabeza; entramos en fuego y en aguas, y sacástenos á hartura.
Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
13 Entraré en tu casa con holocaustos: te pagaré mis votos,
Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
14 Que pronunciaron mis labios, y habló mi boca, cuando angustiado estaba.
alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
15 Holocaustos de cebados te ofreceré, con perfume de carneros: sacrificaré bueyes y machos cabríos. (Selah)
Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. (Sela)
16 Venid, oid todos los que teméis á Dios, y contaré lo que ha hecho á mi alma.
Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
17 A él clamé con mi boca, y ensalzado fué con mi lengua.
Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
18 Si en mi corazón hubiese yo mirado á la iniquidad, el Señor no [me] oyera.
Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
19 Mas ciertamente [me] oyó Dios; antendió á la voz de mi súplica.
amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
20 Bendito Dios, que no echó [de sí] mi oración, ni de mí su misericordia.
Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!

< Salmos 66 >