< Salmos 49 >

1 Al Músico principal: Salmo para los hijos de Coré. OID esto, pueblos todos; escuchad, habitadores todos del mundo:
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku ji wannan, dukanku mutane; ku saurara, dukanku waɗanda suke zama a wannan duniya,
2 Así los plebeyos como los nobles, el rico y el pobre juntamente.
babba da yaro mai arziki da talaka.
3 Mi boca hablará sabiduría; y el pensamiento de mi corazón inteligencia.
Bakina zai yi maganar hikima; magana daga zuciyata za tă ba da ganewa.
4 Acomodaré á ejemplos mi oído: declararé con el arpa mi enigma.
Zan juye kunnena ga karin magana; da garaya zan ƙarfafa kacici-kacicina.
5 ¿Por qué he de temer en los días de adversidad, cuando la iniquidad de mis insidiadores me cercare?
Don me zan ji tsoro sa’ad da mugayen kwanaki suka zo, sa’ad da mugaye masu ruɗu suka kewaye ni,
6 Los que confían en sus haciendas, y en la muchedumbre de sus riquezas se jactan,
waɗanda suka dogara ga arzikinsu suna kuma fariya a kan yawan arzikinsu?
7 Ninguno de [ellos] podrá en manera alguna redimir al hermano, ni dar á Dios su rescate.
Ba wani da zai iya ceton ran wani ko yă ba wa Allah kuɗin fansa saboda shi,
8 (Porque la redención de su vida es de gran precio, y no se hará jamás; )
kuɗin fansa domin rai yana da tsada, babu abin da za a biya da ya taɓa isa,
9 Que viva adelante para siempre, y nunca vea la sepultura.
da zai sa yă ci gaba da rayuwa har abada yă hana shi shigan kabari yă ruɓa.
10 Pues se ve que mueren los sabios, así como el insensato y el necio perecen, y dejan á otros sus riquezas.
Gama kowa na iya ganin masu hikima na mutuwa; wawaye da marasa azanci su ma kan hallaka su bar wa waɗansu arzikinsu.
11 En su interior [tienen] que sus casas [serán] eternas, y sus habitaciones para generación y generación: llamaron sus tierras de sus nombres.
Kaburburansu za su ci gaba da zama gidajensu har abada, Can za su kasance har zamanai marasa ƙarewa, ko da yake sun ba wa filaye sunayen kansu.
12 Mas el hombre no permanecerá en honra: es semejante á las bestias que perecen.
Amma mutum, kome arzikinsa, ba ya dawwama; shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
13 Este su camino es su locura: con todo, corren sus descendientes por el dicho de ellos. (Selah)
Wannan ne ƙaddarar waɗanda suke dogara a kansu, da kuma ta mabiyansu, waɗanda suka tabbatar da faɗinsu. (Sela)
14 Como rebaños serán puestos en la sepultura; la muerte se cebará en ellos; y los rectos se enseñorearán de ellos por la mañana: y se consumirá su bien parecer en el sepulcro de su morada. (Sheol h7585)
Kamar tumaki an ƙaddara su ga kabari; za su kuwa zama abincin mutuwa amma masu gaskiya za su yi mulki a kansu da safe. Kamanninsu za su ruɓe a cikin kabari, nesa da gidajensu masu tsada. (Sheol h7585)
15 Empero Dios redimirá mi vida del poder de la sepultura, cuando me tomará. (Selah) (Sheol h7585)
Amma Allah zai ceci raina daga kabari; tabbatacce zai ɗauke ni zuwa wurinsa. (Sela) (Sheol h7585)
16 No temas cuando se enriquece alguno, cuando aumenta la gloria de su casa;
Kada ka razana da yawa sa’ad da mutum ya yi arziki sa’ad da darajar gidansa ta ƙaru;
17 Porque en muriendo no llevará nada, ni descenderá tras él su gloria.
gama ba zai ɗauki kome tare da shi sa’ad da ya mutu ba, darajarsa ba za tă gangara tare da shi ba.
18 Si bien mientras viviere, dirá dichosa á su alma: y tú serás loado cuando bien te tratares.
Ko da yake yayinda yake a raye ya ɗauka kansa mai albarka ne, mutane kuma sun yabe ka sa’ad da kake cin nasara,
19 Entrará á la generación de sus padres: no verán luz para siempre.
zai gamu da tsarar kakanninsa, waɗanda ba za su taɓa ganin hasken rayuwa ba.
20 El hombre en honra que no entiende, semejante es á las bestias que perecen.
Mutumin da yake da arziki ba tare da ganewa ba shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.

< Salmos 49 >