< Salmos 140 >
1 Al Músico principal: Salmo de David. LÍBRAME, oh Jehová, de hombre malo: guárdame de hombre violento;
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ka cece ni, ya Ubangiji, daga mugaye; ka tsare ni daga mutane masu rikici,
2 Los cuales maquinan males en el corazón, cada día urden contiendas.
masu shirya maƙarƙashiya a zukatansu suna kuma kawo yaƙi kullum.
3 Aguzaron su lengua como la serpiente; veneno de áspid hay debajo de sus labios. (Selah)
Suna sa harsunansu su yi kaifi kamar na maciji; dafin gamsheƙa yana a leɓunansu. (Sela)
4 Guárdame, oh Jehová, de manos del impío, presérvame del hombre injurioso; que han pensado de trastornar mis pasos.
Ka kiyaye ni, ya Ubangiji, daga hannuwan mugaye; ka tsare ni daga mutane masu rikici waɗanda suke shirin kwashe ni a ƙafafu.
5 Hanme escondido lazo y cuerdas los soberbios; han tendido red junto á la senda; me han puesto lazos. (Selah)
Masu girman kai sun sa mini tarko; sun shimfiɗa igiyoyin ragarsu sun kuma shirya mini tarko a hanyata. (Sela)
6 He dicho á Jehová: Dios mío eres tú; escucha, oh Jehová, la voz de mis ruegos.
Ya Ubangiji, na ce maka, “Kai ne Allahna.” Ka ji kukata ta neman jinƙai, ya Ubangiji.
7 Jehová Señor, fortaleza de mi salud, tú pusiste á cubierto mi cabeza el día de las armas.
Ya Ubangiji Mai Iko Duka, mai fansana mai ƙarfi, wanda yake garkuwoyin kaina a ranar yaƙi.
8 No des, oh Jehová, al impío sus deseos; no saques adelante su pensamiento, [que no] se ensoberbezca. (Selah)
Kada ka biya wa mugaye bukatunsu, ya Ubangiji; kada ka bar shirinsu su yi nasara, in ba haka ba za su yi fariya. (Sela)
9 En cuanto á los que por todas partes me rodean, la maldad de sus propios labios cubrirá su cabeza.
Bari kawunan waɗanda suka kewaye ni su rufu da masifun da leɓunansu suka jawo.
10 Caerán sobre ellos brasas; [Dios] los hará caer en el fuego, en profundos hoyos de donde no salgan.
Bari garwashin wuta yă zubo a kansu; bari a jefar da su cikin wuta, cikin rami mai zurfi, kada su sāke tashi.
11 El hombre deslenguado no será firme en la tierra: el mal cazará al hombre injusto para derribarle.
Kada masu ɓata suna su taɓa kahu a ƙasar; bari masifa ta farauci mutane masu rikici.
12 Yo sé que hará Jehová el juicio del afligido, el juicio de los menesterosos.
Na san cewa Ubangiji ya shirya wa matalauta adalci yana kuma yi wa mabukata adalci.
13 Ciertamente los justos alabarán tu nombre; los rectos morarán en tu presencia.
Tabbatacce masu adalci za su yabi sunanka masu aikata gaskiya kuma za su zauna a gabanka.