< Salmos 114 >

1 CUANDO salió Israel de Egipto, la casa de Jacob del pueblo bárbaro,
Sa’ad da Isra’ila ya fito daga Masar, gidan Yaƙub daga mutane masu baƙon harshe,
2 Judá fué su consagrada heredad, Israel su señorío.
Yahuda ya zama wuri mai tsarki na Allah, Isra’ila mallakarsa.
3 La mar vió, y huyó; el Jordán se volvió atrás.
Teku ya kalla ya kuma gudu, Urdun ya juye da baya;
4 Los montes saltaron como carneros: los collados como corderitos.
duwatsu suka yi tsalle kamar raguna, tuddai kamar tumaki.
5 ¿Qué tuviste, oh mar, que huiste? ¿y tú, oh Jordán, que te volviste atrás?
Me ya sa, ya teku, kika gudu, Ya Urdun, ka juya baya,
6 Oh montes, ¿por qué saltasteis como carneros, [y] vosotros, collados, como corderitos?
ku duwatsu, kuka yi tsalle kamar raguna, ku tuddai, kamar tumaki?
7 A la presencia del Señor tiembla la tierra, á la presencia del Dios de Jacob;
Ki yi rawar jiki, ya duniya, a gaban Ubangiji, a gaban Allah na Yaƙub,
8 El cual tornó la peña en estanque de aguas, y en fuente de aguas la roca.
wanda ya juye dutse ya zama tafki, dutse mai ƙarfi zuwa maɓulɓulan ruwa.

< Salmos 114 >