< Salmos 106 >
1 ALELUYA. Alabad á Jehová, porque es bueno; porque para siempre [es] su misericordia.
Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 ¿Quién expresará las valentías de Jehová? ¿[quién] contará sus alabanzas?
Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
3 Dichosos los que guardan juicio, los que hacen justicia en todo tiempo.
Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
4 Acuérdate de mí, oh Jehová, según [tu] benevolencia para con tu pueblo: visítame con tu salud;
Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
5 Para que yo vea el bien de tus escogidos, para que me goce en la alegría de tu gente, y me gloríe con tu heredad.
don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
6 Pecamos con nuestros padres, hicimos iniquidad, hicimos impiedad.
Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
7 Nuestros padres en Egipto no entendieron tus maravillas; no se acordaron de la muchedumbre de tus misericordias; sino que se rebelaron junto á la mar, en el mar Bermejo.
Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
8 Salvólos empero por amor de su nombre, para hacer notoria su fortaleza.
Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
9 Y reprendió al mar Bermejo, y secólo; é hízoles ir por el abismo, como por un desierto.
Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
10 Y salvólos de mano del enemigo, y rescatólos de mano del adversario.
Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
11 Y cubrieron las aguas á sus enemigos: no quedó uno de ellos.
Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
12 Entonces creyeron á sus palabras, y cantaron su alabanza.
Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
13 Apresuráronse, olvidáronse de sus obras; no esperaron en su consejo.
Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
14 Y desearon con ansia en el desierto; y tentaron á Dios en la soledad.
A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
15 Y él les dió lo que pidieron; mas envió flaqueza en sus almas.
Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
16 Tomaron después celo contra Moisés en el campo, [y] contra Aarón el santo de Jehová.
A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
17 Abrióse la tierra, y tragó á Dathán, y cubrió la compañía de Abiram.
Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
18 Y encendióse el fuego en su junta; la llama quemó los impíos.
Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
19 Hicieron becerro en Horeb, y encorváronse á un vaciadizo.
A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
20 Así trocaron su gloria por la imagen de un buey que come hierba.
Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
21 Olvidaron al Dios de su salud, que había hecho grandezas en Egipto;
Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
22 Maravillas en la tierra de Châm, cosas formidables sobre el mar Bermejo.
mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
23 Y trató de destruirlos, á no haberse puesto Moisés su escogido al portillo delante de él, á fin de apartar su ira, para que no [los] destruyese.
Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
24 Empero aborrecieron la tierra deseable: no creyeron á su palabra;
Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
25 Antes murmuraron en sus tiendas, y no oyeron la voz de Jehová.
Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
26 Por lo que alzó su mano á ellos, en orden á postrarlos en el desierto,
Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
27 Y humillar su simiente entre las gentes, y esparcirlos por las tierras.
ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
28 Allegáronse asimismo á Baal-peor, y comieron los sacrificios de los muertos.
Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
29 Y ensañaron [á Dios] con sus obras, y desarrollóse la mortandad en ellos.
suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
30 Entonces se levantó Phinees, é hizo juicio; y se detuvo la plaga.
Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
31 Y fuéle contado á justicia de generación en generación para siempre.
An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
32 También le irritaron en las aguas de Meriba: é hizo mal á Moisés por causa de ellos;
A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
33 Porque hicieron se rebelase su espíritu, como lo expresó con sus labios.
saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
34 No destruyeron los pueblos que Jehová les dijo;
Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
35 Antes se mezclaron con las gentes, y aprendieron sus obras,
amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
36 Y sirvieron á sus ídolos; los cuales les fueron por ruina.
Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
37 Y sacrificaron sus hijos y sus hijas á los demonios;
Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
38 Y derramaron la sangre inocente, la sangre de sus hijos y de sus hijas, que sacrificaron á los ídolos de Canaán: y la tierra fué contaminada con sangre.
Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
39 Contamináronse así con sus obras, y fornicaron con sus hechos.
Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
40 Encendióse por tanto el furor de Jehová sobre su pueblo, y abominó su heredad:
Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
41 Y entrególos en poder de las gentes, y enseñoreáronse de ellos los que los aborrecían.
Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
42 Y sus enemigos los oprimieron, y fueron quebrantados debajo de su mano.
Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
43 Muchas veces los libró; mas ellos se rebelaron á su consejo, y fueron humillados por su maldad.
Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
44 El con todo, miraba cuando estaban en angustia, y oía su clamor:
Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
45 Y acordábase de su pacto con ellos, y arrepentíase conforme á la muchedumbre de sus miseraciones.
saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
46 Hizo asimismo tuviesen de ellos misericordia todos los que los tenían cautivos.
Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
47 Sálvanos, Jehová Dios nuestro, y júntanos de entre las gentes, para que loemos tu santo nombre, para que nos gloriemos en tus alabanzas.
Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
48 Bendito Jehová Dios de Israel, desde el siglo y hasta el siglo: y diga todo el pueblo, Amén. Aleluya.
Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.