< Salmos 102 >
1 Oración del pobre, cuando estuviere angustiado, y delante de Jehová derramare su lamento. JEHOVÁ, oye mi oración, y venga mi clamor á ti.
Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
2 No escondas de mí tu rostro: en el día de mi angustia inclina á mí tu oído; el día que [te] invocare, apresúrate á responderme.
Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
3 Porque mis días se han consumido como humo; y mis huesos cual tizón están quemados.
Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
4 Mi corazón fué herido, y secóse como la hierba; por lo cual me olvidé de comer mi pan.
Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
5 Por la voz de mi gemido mis huesos se han pegado á mi carne.
Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
6 Soy semejante al pelícano del desierto; soy como el buho de las soledades.
Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
7 Velo, y soy como el pájaro solitario sobre el tejado.
Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
8 Cada día me afrentan mis enemigos; los que se enfurecen contra mí, hanse contra mí conjurado.
Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
9 Por lo que como la ceniza á manera de pan, y mi bebida mezclo con lloro,
Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
10 A causa de tu enojo y de tu ira; pues me alzaste, y me has arrojado.
saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
11 Mis días son como la sombra que se va; y heme secado como la hierba.
Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
12 Mas tú, Jehová, permanecerás para siempre, y tu memoria para generación y generación.
Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
13 Tú levantándote, tendrás misericordia de Sión; porque el tiempo de tener misericordia de ella, porque el plazo es llegado.
Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
14 Porque tus siervos aman sus piedras, y del polvo de ella tienen compasión.
Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
15 Entonces temerán las gentes el nombre de Jehová, y todos los reyes de la tierra tu gloria;
Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
16 Por cuanto Jehová habrá edificado á Sión, y en su gloria será visto;
Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
17 Habrá mirado á la oración de los solitarios, y no habrá desechado el ruego de ellos.
Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
18 Escribirse ha esto para la generación venidera: y el pueblo que se criará, alabará á JAH.
Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
19 Porque miró de lo alto de su santuario; Jehová miró de los cielos á la tierra,
“Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
20 Para oir el gemido de los presos, para soltar á los sentenciados á muerte;
don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
21 Porque cuenten en Sión el nombre de Jehová, y su alabanza en Jerusalem,
Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
22 Cuando los pueblos se congregaren en uno, y los reinos, para servir á Jehová.
sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
23 El afligió mi fuerza en el camino; acortó mis días.
Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
24 Dije: Dios mío, no me cortes en el medio de mis días: por generación de generaciones son tus años.
Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
25 Tú fundaste la tierra antiguamente, y los cielos son obra de tus manos.
A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
26 Ellos perecerán, y tú permanecerás; y todos ellos como un vestido se envejecerán; como una ropa de vestir los mudarás, y serán mudados:
Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
27 Mas tú eres el mismo, y tus años no se acabarán.
Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
28 Los hijos de tus siervos habitarán, y su simiente será afirmada delante de ti.
’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”