< Job 6 >

1 Y RESPONDIÓ Job y dijo:
Sa’an nan Ayuba ya amsa,
2 ¡Oh si pesasen al justo mi queja y mi tormento, y se alzasen igualmente en balanza!
“Da kawai za a iya auna wahalata a kuma sa ɓacin raina a ma’auni!
3 Porque pesaría aquél más que la arena del mar: y por tanto mis palabras son cortadas.
Ba shakka da sun fi yashin teku nauyi, shi ya sa nake magana haka.
4 Porque las saetas del Todopoderoso están en mí, cuyo veneno bebe mi espíritu; y terrores de Dios me combaten.
Kibiyoyin Maɗaukaki suna a kaina, ruhuna yana shan dafinsa; fushin Allah ya sauka a kaina.
5 ¿Acaso gime el asno montés junto á la hierba? ¿muge el buey junto á su pasto?
Jaki yakan yi kuka sa’ad da ya sami ciyawar ci, ko saniya takan yi kuka in ta sami abincinta?
6 ¿Comeráse lo desabrido sin sal? ¿ó habrá gusto en la clara del huevo?
Akan cin abinci marar ɗanɗano ba tare da an sa gishiri ba, ko akwai wani ƙanshin daɗi a cikin farin ruwan ƙwai?
7 Las cosas que mi alma no quería tocar, por los dolores son mi comida.
Na ƙi in taɓa shi; irin wannan abinci zai sa ni rashin lafiya.
8 ¡Quién me diera que viniese mi petición, y que Dios [me] otorgase lo que espero;
“Kash, da ma Allah zai ba ni abin da nake fatar samu, da ma Allah zai biya mini bukatata,
9 Y que pluguiera á Dios quebrantarme; que soltara su mano, y me deshiciera!
wato, Allah yă kashe ni, yă miƙa hannunsa yă yanke raina!
10 Y sería aún mi consuelo, si me asaltase con dolor sin dar más tregua, que yo no he escondido las palabras del Santo.
Da sai in ji daɗi duk zafin da nake sha ban hana maganar Mai Tsarkin nan cika ba.
11 ¿Cuál es mi fortaleza para esperar aún? ¿y cuál mi fin para dilatar mi vida?
“Wane ƙarfi nake da shi, har da zan ci gaba da sa zuciya? Wane sa zuciya ne zai sa in yi haƙuri?
12 ¿Es mi fortaleza la de las piedras? ¿ó mi carne, es de acero?
Da ƙarfin dutse aka yi ni ne? Ko jikina tagulla ne?
13 ¿No me ayudo cuanto puedo, y el poder me falta del todo?
Ina da wani ikon da zan iya taimakon kai na ne, yanzu da aka kore nasara daga gare ni?
14 El atribulado es consolado de su compañero: mas hase abandonado el temor del Omnipotente.
“Duk wanda ya ƙi yă yi alheri ga aboki ya rabu ta tsoron Maɗaukaki.
15 Mis hermanos han mentido cual arroyo: pasáronse como corrientes impetuosas,
Amma’yan’uwana sun nuna ba zan iya dogara gare su ba, kamar rafin da yakan bushe da rani,
16 Que están escondidas por la helada, y encubiertas con nieve;
kamar rafin da yakan cika a lokacin ƙanƙara, yă kuma kumbura kamar ƙanƙarar da ta narke,
17 Que al tiempo del calor son deshechas, y en calentándose, desaparecen de su lugar;
amma da rani sai yă bushe, lokacin zafi ba a samun ruwa yana gudu a wurin.
18 Apártanse de la senda de su rumbo, van menguando y piérdense.
Ayari sukan bar hanyarsu; sukan yi ta neman wurin da za su sami ruwa, su kāsa samu har su mutu.
19 Miraron los caminantes de Temán, los caminantes de Saba esperaron en ellas:
Ayarin Tema sun nemi ruwa, matafiya’yan kasuwa Sheba sun nema cike da begen samu.
20 [Mas] fueron avergonzados por su esperanza; porque vinieron hasta ellas, y halláronse confusos.
Ransu ya ɓace, domin sun sa zuciya sosai; sa’ad da suka kai wurin kuwa ba su sami abin da suka sa zuciyar samu ba.
21 Ahora ciertamente como ellas sois vosotros: que habéis visto el tormento, y teméis.
Yanzu kuma kun nuna mini ba ku iya taimako; kun ga abin bantsoro kuka tsorata.
22 ¿Os he dicho yo: Traedme, y pagad por mí de vuestra hacienda;
Ko na taɓa cewa, ‘Ku ba da wani abu a madadina, ko na roƙe ku, ku ba da wani abu domina daga cikin dukiyarku,
23 Y libradme de la mano del opresor, y redimidme del poder de los violentos?
ko kuma kun taɓa kuɓutar da ni daga hannun maƙiyina, ko kun taɓa ƙwato ni daga hannun marasa kirki’?
24 Enseñadme, y yo callaré: y hacedme entender en qué he errado.
“Ku koya mini, zan yi shiru; ku nuna mini inda ban yi daidai ba.
25 ¡Cuán fuertes son las palabras de rectitud! Mas ¿qué reprende el que reprende de vosotros?
Faɗar gaskiya tana da zafi! Amma ina amfanin gardamar da kuke yi?
26 ¿Pensáis censurar palabras, y los discursos de un desesperado, que son como el viento?
Ko kuna so ku gyara abin da na faɗi ne, ku mai da magana wanda yake cikin wahala ta zama ta wofi?
27 También os arrojáis sobre el huérfano, y hacéis hoyo delante de vuestro amigo.
Kukan yi ƙuri’a a kan marayu ku kuma sayar da abokinku.
28 Ahora pues, si queréis, mirad en mí, y [ved] si miento delante de vosotros.
“Amma yanzu ku dube ni da kyau, zan yi muku ƙarya ne?
29 Tornad ahora, y no haya iniquidad; volved aún [á considerar] mi justicia en esto.
Ku bi a hankali, kada ku ɗora mini laifi; ku sāke dubawa, gama ba ni da laifi.
30 ¿Hay iniquidad en mi lengua? ¿no puede mi paladar discernir las cosas depravadas?
Ko akwai wata mugunta a bakina? Bakina ba zai iya rarrabewa tsakanin gaskiya da ƙarya ba?

< Job 6 >