< Job 37 >

1 A ESTO también se espanta mi corazón, y salta de su lugar.
“Wannan ya sa gabana ya fāɗi, zuciyata ta yi tsalle.
2 Oid atentamente su voz terrible, y el sonido que sale de su boca.
Ka saurara! Ka saurari rurin muryarsa, tsawar da take fita daga bakinsa.
3 Debajo de todos los cielos lo dirige, y su luz hasta los fines de la tierra.
Ya saki walƙiyarsa, a ƙarƙashin dukan sammai ya kuma aika ta ko’ina a cikin duniya.
4 Después de ella bramará el sonido, tronará él con la voz de su magnificencia; y aunque sea oída su voz, no los detiene.
Bayan wannan sai ƙarar rurinsa ta biyo; Ya tsawata da muryarsa mai girma. Sa’ad da ya sāke yin tsawa ba ya rage wani abu.
5 Tronará Dios maravillosamente con su voz; él hace grandes cosas, que nosotros no entendemos.
Muryar Allah tana tsawatawa a hanyoyi masu ban al’ajabi; yana yin manyan abubuwa waɗanda sun wuce ganewarmu.
6 Porque á la nieve dice: Desciende á la tierra; también á la llovizna, y á los aguaceros de su fortaleza.
Yakan ce wa dusar ƙanƙara, ‘Fāɗo a kan duniya,’ ya kuma ce wa ruwa, ‘Zubo da ƙarfi.’
7 Así hace retirarse á todo hombre, para que los hombres todos reconozcan su obra.
Domin dukan mutanen da ya halitta za su san aikinsa, ya hana kowane mutum yin wahalar aiki.
8 La bestia se entrará en su escondrijo, y estaráse en sus moradas.
Dabbobi sun ɓoye; sun zauna cikin kogunansu.
9 Del mediodía viene el torbellino, y el frío de los vientos del norte.
Guguwa tana fitowa daga inda take, sanyi kuma daga iska mai sanyi.
10 Por el soplo de Dios se da el hielo, y las anchas aguas son constreñidas.
Da numfashinsa Allah yana samar da ƙanƙara sai manyan ruwaye su zama ƙanƙara.
11 Regando también llega á disipar la densa nube, y con su luz esparce la niebla.
Yana cika gizagizai da lema; yana baza walƙiyarsa ta cikinsu.
12 Asimismo por sus designios se revuelven las nubes en derredor, para hacer sobre la haz del mundo, en la tierra, lo que él les mandara.
Bisa ga bishewarsa suke juyawa a kan fuskar duniya, suna yin dukan abin da ya umarce su su yi.
13 Unas veces por azote, otras por causa de su tierra, otras por misericordia las hará parecer.
Yana aiko da ruwa domin horon mutane, ko kuma don yă jiƙa duniya yă kuma nuna ƙaunarsa.
14 Escucha esto, Job; repósate, y considera las maravillas de Dios.
“Ka saurari wannan Ayuba; ka tsaya ka dubi abubuwan al’ajabi na Allah.
15 ¿Supiste tú cuándo Dios las ponía en concierto, y hacía levantar la luz de su nube?
Ko ka san yadda Allah yake iko da gizagizai ya kuma sa walƙiyarsa ta haskaka?
16 ¿Has tú conocido las diferencias de las nubes, las maravillas del Perfecto en sabiduría?
Ko ka san yadda gizagizai suke tsayawa cik a sararin sama, waɗannan abubuwa al’ajabi na mai cikakken sani.
17 ¿Por qué están calientes tus vestidos cuando se fija el [viento del] mediodía sobre la tierra?
Kai mai sa kaya don ka ji ɗumi lokacin da iska mai sanyi take hurawa,
18 ¿Extendiste tú con él los cielos, firmes como un espejo sólido?
ko za ka iya shimfiɗa sararin sama tare da shi da ƙarfi kamar madubi?
19 Muéstranos qué le hemos de decir; [porque] nosotros no podemos componer [las ideas] á causa de las tinieblas.
“Gaya mana abin da ya kamata mu ce masa; ba za mu iya kawo ƙara ba domin duhunmu.
20 ¿Será preciso contarle cuando yo hablaré? Por más que el hombre razone, quedará como abismado.
Ko za a gaya masa cewa ina so in yi magana? Ko wani zai nemi a haɗiye shi?
21 He aquí aún: no se puede mirar la luz esplendente en los cielos, luego que pasa el viento y los limpia,
Yanzu ba wanda zai iya kallon rana, yadda take da haske a sararin sama bayan iska ta share ta.
22 Viniendo de la parte del norte la dorada claridad. En Dios hay una majestad terrible.
Yana fitowa daga arewa da haske na zinariya, Allah yana zuwa da ɗaukaka mai ban al’ajabi.
23 El [es] Todopoderoso, al cual no alcanzamos, grande en potencia; y en juicio y en multitud de justicia no afligirá.
Maɗaukaki ya fi ƙarfin ganewarmu, shi babban mai iko ne, mai gaskiya da babban adalci, ba ya cutar mutum.
24 Temerlo han por tanto los hombres: él no mira á los sabios de corazón.
Saboda haka, mutane suke girmama shi, ko bai kula da waɗanda suke gani su masu hikima ba ne?”

< Job 37 >