< Job 10 >
1 ESTÁ mi alma aburrida de mi vida: daré yo suelta á mi queja sobre mí, hablaré con amargura de mi alma.
“Na gaji da rayuwa; saboda haka bari in faɗi zuciyata gabagadi yadda raina yake jin ba daɗi.
2 Diré á Dios: no me condenes; hazme entender por qué pleiteas conmigo.
Zan ce wa Allah, kada ka hukunta ni, amma ka gaya mini laifin da na yi maka.
3 ¿Parécete bien que oprimas, que deseches la obra de tus manos, y que resplandezcas sobre el consejo de los impíos?
Kana jin daɗin ba ni wahala, don me ka yashe ni, abin da ka halitta da hannunka, yayinda kake murmushi game da shirye-shiryen mugaye?
4 ¿Tienes tú ojos de carne? ¿ves tú como ve el hombre?
Idanunka irin na mutum ne? Kana gani yadda mutum yake gani ne?
5 ¿Son tus días como los días del hombre, ó tus años como los tiempos humanos,
Kwanakinka kamar na mutane ne, ko shekarunka kamar na mutane ne
6 Para que inquieras mi iniquidad, y busques mi pecado,
da za ka neme ni da laifi ka hukunta ni?
7 Sobre saber tú que no soy impío, y que no hay quien de tu mano libre?
Ko da yake ka san ba ni da laifi, kuma ba wanda zai iya cetona daga hannunka.
8 Tus manos me formaron y me compusieron todo en contorno: ¿y así me deshaces?
“Da hannuwanka ka ƙera ni, kai ka halicce ni. Yanzu kuma kai za ka juya ka hallaka ni?
9 Acuérdate ahora que como á lodo me diste forma: ¿y en polvo me has de tornar?
Ka tuna cewa ka mulmula ni kamar yumɓu. Yanzu za ka mai da ni in zama ƙura kuma?
10 ¿No me fundiste como leche, y como un queso me cuajaste?
Ba kai ka zuba ni kamar madara ba, na daskare kamar cuku.
11 Vestísteme de piel y carne, y cubrísteme de huesos y nervios.
Ka rufe ni da tsoka da fata, ka harhaɗa ni da ƙasusuwa da jijiyoyi?
12 Vida y misericordia me concediste, y tu visitación guardó mi espíritu.
Ka ba ni rai ka kuma yi mini alheri, kuma cikin tanadinka ka kula da ruhuna.
13 Y estas cosas tienes guardadas en tu corazón; yo sé que esto está cerca de ti.
“Amma wannan shi ne abin da ka ɓoye a zuciyarka, na kuma san abin da yake cikin zuciyarka ke nan.
14 Si pequé, tú me has observado, y no me limpias de mi iniquidad.
In na yi zunubi kana kallo na kuma ba za ka fasa ba ni horo ba don laifin da na yi.
15 Si fuere malo, ¡ay de mí! y si fuere justo, no levantaré mi cabeza, estando harto de deshonra, y de verme afligido.
Idan ina da laifi, kaitona! Ko da ba ni da laifi, ba zan iya ɗaga fuskata ba, gama kunya ta ishe ni duk ɓacin rai ya ishe ni.
16 Y subirá de punto, [pues] me cazas como á león, y tornas á hacer en mí maravillas.
In na ɗaga kaina, za ka neme ni kamar zaki ka sāke nuna al’ajabin ikonka a kaina.
17 Renuevas contra mí tus plagas, y aumentas conmigo tu furor, remudándose sobre mí ejércitos.
Kana sāke kawo sababbin waɗanda za su ba da shaida a kaina kana ƙara haushinka a kaina; kana ƙara kawo mini hari.
18 ¿Por qué me sacaste de la matriz? Habría yo espirado, y no me vieran ojos.
“Me ya sa ka fito da ni daga cikin uwata? Da ma na mutu kafin a haife ni.
19 Fuera, como si nunca hubiera sido, llevado desde el vientre á la sepultura.
Da ma ba a halicce ni ba, da na mutu tun daga cikin cikin uwata na wuce zuwa kabari!
20 ¿No son mis días poca cosa? Cesa pues, y déjame, para que me conforte un poco.
’Yan kwanakina ba su kusa ƙarewa ba ne? Ka rabu da ni don in ɗan samu sukuni na ɗan lokaci
21 Antes que vaya para no volver, á la tierra de tinieblas y de sombra de muerte;
kafin in koma inda na fito, ƙasa mai duhu da inuwa sosai,
22 Tierra de oscuridad, lóbrega como sombra de muerte, sin orden, y que aparece como [la] oscuridad [misma].
zuwa ƙasa mai duhun gaske, da inuwa da hargitsi, inda haske yake kamar duhu.”