< Salmos 88 >

1 Jehová Dios de mi salud, día y noche clamo delante de ti.
Waƙa ce, Zabura ta’ya’yan Kora maza. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat leyannotmaskil na Heman dangin Ezra. Ya Ubangiji, Allah wanda ya cece ni, dare da rana ina kuka a gabanka.
2 Entre delante de ti mi oración: inclina tu oído a mi clamor.
Bari addu’ata ta zo a gabanka; ka kasa kunne ga kukata.
3 Porque mi alma está harta de males: y mi vida ha llegado a la sepultura. (Sheol h7585)
Gama raina yana cike da wahala rayuwata tana gab da kabari. (Sheol h7585)
4 Soy contado con los que descienden al sepulcro: soy como hombre sin fuerza;
An lissafta ni cikin waɗanda suka gangara zuwa cikin rami; ni kamar mutumin da ba shi da ƙarfi ne.
5 Librado entre los muertos. Como los matados que duermen en el sepulcro: que no te acuerdas más de ellos, y que son cortados de tu mano.
An ware ni tare da matattu, kamar waɗanda aka kashe da suke kwance a kabari, waɗanda ba ka ƙara tunawa, waɗanda aka yanke daga taimakonka.
6 Hásme puesto en el hoyo profundo: en tinieblas, en honduras.
Ka sa ni a ramin da yake can ƙasa cikin zurfafa mafi duhu.
7 Sobre mí se ha acostado tu ira: y con todas tus ondas me has afligido. (Selah)
Hasalarka tana da nauyi a kaina; ka turmushe ni da dukan raƙumanka. (Sela)
8 Has alejado de mí mis conocidos: hásme puesto a ellos por abominaciones: estoy encerrado, y no saldré.
Ka ɗauke abokaina na kurkusa daga gare ni ka sa na zama abin ƙyama a gare su. An kange ni, ba yadda zan kuɓuta
9 Mis ojos enfermaron a causa de mi aflicción: te he llamado, o! Jehová, cada día he extendido a ti mis manos.
idanuna ba sa gani sosai saboda baƙin ciki. Ina kira gare ka, ya Ubangiji, kowace rana; na tā da hannuwana zuwa gare ka.
10 ¿Harás milagro a los muertos? ¿Levantarse han los muertos para alabarte? (Selah)
Kakan nuna wa matattu ayyukanka na banmamaki ne? Waɗanda suka mutu sukan tashi su yabe ka ne? (Sela)
11 ¿Será contada en el sepulcro tu misericordia? ¿tu verdad en la perdición?
Ana furta ƙaunar a cikin kabari ne, ana zancen amincinka a cikin Hallaka ne?
12 ¿Será conocida en las tinieblas tu maravilla? ¿y tu justicia en la tierra del olvido?
An san ayyukanka masu banmamaki a wurin duhu ne, ko ayyukan adalcinka a lahira?
13 Y yo a ti, o! Jehová, he clamado: y de mañana te previno mi oración.
Amma ina kuka gare ka neman taimako, ya Ubangiji; da safe addu’ata kan zo gabanka.
14 ¿Por qué, o! Jehová, desechas a mi alma? ¿ por qué escondes tu rostro de mí?
Don me, ya Ubangiji, ka ƙi ni ka kuma ɓoye fuskarka daga gare ni?
15 Yo soy afligido y menesteroso: desde la mocedad he llevado tus temores, he estado medroso.
Tun ina ƙarami na sha wahala na kuma yi kusa in mutu; na sha wahalar razanarka kuma na kuma fid da zuciya.
16 Sobre mí han pasado tus iras; tus espantos me han cortado.
Hasalarka ta sha kaina; razanarka ta hallaka ni.
17 Hánme rodeado como aguas de continuo: hánme cercado a una.
Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa; sun mamaye ni ɗungum.
18 Has alejado de mí el amigo y el compañero; y mis conocidos en las tinieblas.
Ka ɗauke abokaina da ƙaunatattuna daga gare ni; duhu ne abokina na kurkusa.

< Salmos 88 >