< Salmos 81 >
1 Cantád a Dios nuestra fortaleza: cantád con júbilo al Dios de Jacob.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Ta Asaf. Ku rera don farin ciki ga Allah ƙarfinmu; ku yi sowa ga Allah na Yaƙub!
2 Tomád la canción, y dad al adufe: a la arpa de alegría, con el salterio.
Ku fara kaɗe-kaɗe, ku buga ganga, ku kaɗa garaya da molo masu daɗi.
3 Tocád la trompeta en la nueva luna, en el día señalado: en el día de nuestra solemnidad.
Ku busa ƙahon rago a Sabon Wata, da kuma sa’ad da wata ya kai tsakiya, a ranar Bikinmu;
4 Porque estatuto es de Israel: juicio del Dios de Jacob.
wannan ƙa’ida ce domin Isra’ila, farilla ta Allah na Yaƙub.
5 Por testimonio en José le ha constituido, cuando salió sobre la tierra de Egipto: donde oí lenguaje que no entendía.
Ya kafa shi a matsayin ƙa’ida domin Yusuf sa’ad da ya fito daga Masar. Muka ji yaren da ba mu fahimta ba.
6 Quité entonces su hombro de debajo de la carga: sus manos se quitaron de las ollas.
Ya ce, “Na kau da nauyi daga kafaɗunku; an’yantar da hannuwansu daga kwando.
7 En la angustia llamaste, y yo te libré; te respondí en el secreto del trueno; te probé sobre las aguas de Meriba. (Selah)
Cikin damuwarku kun yi kira na kuwa kuɓutar da ku, na amsa muku daga girgijen tsawa; na gwada ku a ruwan Meriba. (Sela)
8 Oye, pueblo mío, y protestarte he: Israel, si me oyeres;
“Ku ji, ya mutanena, zan kuwa gargaɗe ku, in ba za ku saurare ni ba, ya Isra’ila!
9 No habrá en ti dios ajeno: ni te encorvarás a dios extraño.
Kada ku kasance da baƙon allah a cikinku; ba za ku rusuna ga baƙon allah ba.
10 Yo soy Jehová tu Dios, que te hice subir de la tierra de Egipto: ensancha tu boca, y henchirla he.
Ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya fitar da ku daga Masar. Ku buɗe bakinku zan kuwa cika shi.
11 Mas mi pueblo no oyó mi voz: e Israel no me quiso a mí.
“Amma mutanena ba su saurare ni ba; Isra’ila bai miƙa kansa gare ni ba.
12 Y dejélos a la dureza de su corazón; caminaron en sus consejos.
Saboda haka na ba da su ga zukatansu da suka taurare don su bi dabararsu.
13 ¡O si mi pueblo me oyera, si Israel anduviera en mis caminos!
“A ce mutanena za su saurare ni, a ce Isra’ila zai bi hanyoyina,
14 En nada derribara yo a sus enemigos: y volviera mi mano sobre sus adversarios.
da nan da nan sai in rinjayi abokan gābansu in kuma juye hannuna a kan maƙiyansu!
15 Los aborrecedores de Jehová le hubieran mentido: y el tiempo de ellos fuera para siempre.
Waɗanda suke ƙin Ubangiji za su fāɗi a gabansa da rawar jiki, hukuncinsu kuma zai dawwama har abada.
16 Y Dios le hubiera mantenido de grosura de trigo: y de miel de la piedra te hubiera hartado.
Amma za a ciyar da ku da alkama mafi kyau; da zuma daga dutsen da zai ƙosar da ku.”