< Salmos 69 >

1 Sálvame, o! Dios, porque las aguas han entrado hasta el alma.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin.” Ta Dawuda. Ka cece ni, ya Allah, gama ruwa ya kai wuyata
2 Estoy zabullido en cieno profundo, que no hay pie; soy venido en profundos de aguas, y la corriente me ha anegado.
Na nutse cikin laka mai zurfi, inda babu wurin tsayawa. Na shiga cikin ruwaye masu zurfi; rigyawa ya sha kaina.
3 He trabajado llamando; mi garganta se ha enronquecido; han desfallecido mis ojos de esperar a mi Dios.
Na gaji da kira ina neman taimako; maƙogwarona ya bushe idanuna sun dushe, suna neman Allahna.
4 Hánse aumentado más que los cabellos de mi cabeza los que me aborrecen sin causa; hánse fortalecido mis enemigos, los que me destruyen sin porqué: lo que no hurté, entonces lo volví.
Waɗanda suke ƙina ba dalili sun fi gashin kaina yawa; da yawa ne abokan gābana babu dalili, su da suke nema su hallaka ni. An tilasta mini in mayar da abin da ban sata ba.
5 Dios, tú sabes mi insensatez; y mis delitos no te son ocultos.
Ka san wautata, ya Allah; laifina ba a ɓoye yake daga gare ka ba.
6 No sean avergonzados por mí, los que te esperan, Señor Jehová de los ejércitos; no sean confusos por mí los que te buscan, o! Dios de Israel.
Bari waɗanda suke sa zuciya gare ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki; bari waɗanda suke neman ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Allah na Isra’ila.
7 Porque por ti he sufrido vergüenza; confusión ha cubierto mi rostro.
Gama na jimre da ba’a saboda kai, kunya kuma ta rufe fuskata.
8 He sido extrañado de mis hermanos, y extraño a los hijos de mi madre.
Ni baƙo ne a cikin’yan’uwana, bare kuma ga’ya’yan mahaifiyata maza;
9 Porque el zelo de tu casa me comió, y los denuestos de los que te denuestan, cayeron sobre mí.
gama himma da nake yi wa gidanka yana ƙunata, kuma zagi na masu zaginka yana fāɗuwa a kaina.
10 Y lloré con ayuno de mi alma, y esto me ha sido por afrenta.
Sa’ad da na yi kuka na kuma yi azumi dole in jimre da ba’a;
11 Y puse saco por mi vestido, y fui a ellos por proverbio.
sa’ad da na sanya rigunan makoki, mutane suna maishe ni abin dariya.
12 Hablaban contra mí los que se sentaban a la puerta, y en las canciones de los bebedores de sidra.
Masu zama a ƙofa suna mini ba’a, na zama waƙa a bakin bugaggu da giya.
13 Y yo enderazaba mi oración a ti, o! Jehová, al tiempo de la buena voluntad: o! Dios, por la multitud de tu misericordia óyeme, por la verdad de tu salud.
Amma na yi addu’a gare ka, ya Ubangiji, a lokacin da ka ga dama; a cikin ƙaunarka mai girma, ya Allah, ka amsa mini da tabbacin ceto.
14 Escápame del lodo, y no sea yo anegado; y sea yo librado de los que me aborrecen, y de los profundos de las aguas.
Ka fid da ni daga laka, kada ka bari in nutse; ka cece ni daga waɗanda suke ƙina, daga rurin ruwaye.
15 No me anegue el ímpetu de las aguas, ni me suerba la hondura, ni el pozo cierre sobre mí su boca.
Kada ka bar rigyawa yă sha kaina ko zurfafa su haɗiye ni ko rami yă rufe bakinsa a kaina.
16 Oyeme, Jehová; porque benigna es tu misericordia: conforme a la multitud de tus miseraciones mira por mí.
Ka amsa mini, ya Ubangiji cikin alherin ƙaunarka; cikin jinƙanka mai girma ka juyo gare ni.
17 Y no escondas tu rostro de tu siervo; porque estoy angustiado; apresúrate, óyeme.
Kada ka ɓoye fuskarka daga bawanka; ka amsa mini da sauri, gama ina cikin wahala.
18 Acércate a mi alma, redímela: por causa de mis enemigos líbrame.
Ka zo kusa ka kuɓutar da ni; ka fanshe ni saboda maƙiyana.
19 Tú sabes mi afrenta, y mi confusión, y mi vergüenza; delante de ti están todos mis enemigos.
Ka san yadda ake mini ba’a, ake kunyatar da ni da kuma yadda nake shan kunya; dukan abokan gābana suna a gabanka.
20 La afrenta ha quebrantado mi corazón; y he tenido dolor; y he esperado quien se compadeciese de mí, y no lo hubo, y consoladores, y no hallé.
Ba’a ta sa zuciyata ta karai ta bar ni ba mataimaki; Na nemi a ji tausayina, amma ban sami ko ɗaya ba, na nemi masu ta’aziyya, amma ban sami ko ɗaya ba.
21 Y pusieron en mi comida hiel; y en mi sed me dieron a beber vinagre.
Sun sa abin ɗaci cikin abincina suka kuma ba ni ruwan inabi mai tsami sa’ad da nake jin ƙishi.
22 Sea su mesa delante de ellos por lazo; y lo que es por paces, les sea por tropezón.
Bari teburin da aka shirya a gabansu yă zama musu tarko; bari yă zama sakamakon laifi da kuma tarko.
23 Sean oscurecidos sus ojos para ver; y haz siempre titubear sus lomos.
Bari idanunsu yă dushe don kada su gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.
24 Derrama sobre ellos tu ira, y el furor de tu enojo les comprenda.
Ka kwarara fushinka a kansu; bari fushinka mai zafi yă ci musu.
25 Sea su palacio asolado; en sus tiendas no haya morador.
Bari wurinsu yă zama kufai; kada ka bar wani yă zauna a tentunansu.
26 Porque persiguieron al que tú heriste: y cuentan del dolor de los que tú mataste.
Gama sun tsananta wa waɗanda ka hukunta suna kuma taɗin wahalar waɗanda ka ji musu rauni.
27 Pon maldad sobre su maldad, y no entren en tu justicia.
Ka neme su da laifi a kan laifi; kada ka bar su su sami rabo a cikin cetonka.
28 Sean raídos del libro de los vivientes: y no sean escritos con los justos.
Bari a shafe su sarai daga littafin rai kada a kuma lissafta su tare da adalai.
29 Y yo afligido, y dolorido: tu salud, o! Dios, me defenderá.
Ina cikin zafi da kuma azaba; bari cetonka, ya Allah, yă tsare ni.
30 Yo alabaré el nombre de Dios con canción; y magnificarle he con alabanza.
Zan yabe sunan Allah cikin waƙa in kuma ɗaukaka shi tare wurin yin godiya.
31 Y agradará a Jehová más que buey, y becerro, que echa cuernos y uñas.
Wannan zai gamshi Ubangiji fiye da saniya, fiye da bijimi da ƙahoninsa da kuma kofatansa.
32 Verán los humildes, y regocijarse han: buscád a Dios, y vivirá vuestro corazón.
Matalauta za su gani su kuma yi murna, ku da kuke neman Allah, bari zukatanku su rayu!
33 Porque Jehová oye a los menesterosos, y no menosprecia a sus prisioneros.
Ubangiji yakan ji masu bukata ba ya kuwa ƙyale kamammun mutanensa.
34 Alábenle los cielos y la tierra, las mares y todo lo que se mueve en ellas.
Bari sama da ƙasa su yabe shi, tekuna da dukan abin da yake motsi a cikinsu,
35 Porque Dios guardará a Sión, y reedificará las ciudades de Judá, y habitarán allí, y heredarla han.
gama Allah zai cece Sihiyona yă sāke gina biranen Yahuda. Sa’an nan mutane za su zauna a can su mallake ta,
36 Y la simiente de sus siervos la heredará; y los que aman su nombre habitarán en ella.
’ya’yan bayinsa za su gāje ta, waɗanda kuma suna ƙaunar sunansa za su zauna a can.

< Salmos 69 >