< Salmos 63 >

1 Dios, Dios mío eres tú, a ti madrugaré: mi alma tuvo sed de ti, mi carne te desea en tierra de sequedad, y sequiosa sin aguas.
Zabura ta Dawuda. Sa’ad da yake a hamadar Yahuda. Ya Allah, kai ne Allahna, da nacewa na neme ka; raina yana ƙishinka, jikina yana marmarinka, cikin busasshiyar ƙasar da ta zozaye inda babu ruwa.
2 Así te miré en el santuario, para ver tu fortaleza y tu gloria.
Na gan ka a wuri mai tsarki na kuma dubi ikonka da ɗaukakarka.
3 Porque mejor es tu misericordia que la vida: mis labios te alabarán.
Domin ƙaunarka ta fi rai kyau, leɓunana za su ɗaukaka ka.
4 Así te bendeciré en mi vida: en tu nombre alzaré mis manos.
Zan yabe ka muddin raina, kuma a cikin sunanka zai ɗaga hannuwana.
5 Como de meollo y de grosura será harta mi alma: y con labios de alegría te alabará mi boca,
Raina zai ƙoshi kamar da abinci mafi kyau; da leɓunan rerawa bakina zai yabe ka.
6 Cuando me acordaré de ti en mis camas, cuando a las alboradas meditaré de ti;
A gadona na tuna da kai; ina tunaninka dukan dare.
7 Porque has sido mi socorro: y en la sombra de tus alas me regocijaré.
Domin kai ne mai taimakona, ina rera a cikin inuwar fikafikanka.
8 Mi alma se apegó a ti: tu diestra me ha sustentado.
Raina ya manne maka; hannunka na dama yana riƙe da ni.
9 Mas ellos para destrucción buscaron mi alma: descendieron en lo más bajo de la tierra.
Su da suke neman raina za su hallaka; za su gangara zuwa zurfafan duniya.
10 Matarlos han a filo de espada: porción de zorras serán.
Za a bayar da su ga takobi su kuma zama abincin karnukan jeji.
11 Y el rey se alegrará en Dios, será alabado cualquiera que jura por él: porque la boca de los que hablan mentira, será cerrada.
Amma sarki zai yi farin ciki ga Allah; dukan waɗanda suke rantse da sunan Allah za su yabe shi, amma za a rufe bakunan maƙaryata.

< Salmos 63 >