< Salmos 61 >

1 Oye, o! Dios, mi clamor; está atento a mi oración.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Ta Dawuda. Ka ji kukata, ya Allah; ka saurari addu’ata.
2 Desde el cabo de la tierra clamaré a ti, cuando desmayare mi corazón; a la peña más alta que yo, llévame.
Daga iyakar duniya na yi kira gare ka, na yi kira yayinda zuciyata ta karai; ka bishe ni zuwa dutsen da ya fi ni tsayi.
3 Porque tú has sido mi refugio; torre de fortaleza delante del enemigo.
Gama kai ne mafakata, hasumiya mai ƙarfi gāba da maƙiyi.
4 Yo habitaré en tu tabernáculo para siempre; estaré seguro en el escondedero de tus alas.
Ina marmari in zauna a tentinka har abada in sami mafaka a cikin inuwar fikafikanka. (Sela)
5 Porque tú, o! Dios, has oído mis votos; has dado heredad a los que temen tu nombre.
Gama ka ji alkawarina, ya Allah; ka ba ni gādo na waɗanda suke tsoron sunanka.
6 Días sobre días añadirás al rey: sus años serán como generación y generación.
Ka ƙara kwanakin ran sarki, shekarunsa su kasance a zamanai masu yawa.
7 El estará para siempre delante de Dios; misericordia y verdad apercibe que le conserven.
Bari yă yi mulki a gaban Allah har abada; ka sa ƙaunarka da amincinka su tsare shi.
8 Así cantaré tu nombre para siempre, pagando mis votos cada día.
Sa’an nan zan riƙa rera yabo ga sunanka in kuma cika alkawarina kowace rana.

< Salmos 61 >