< Salmos 60 >

1 Dios, desechástenos, disipástenos; airástete, vuélvete a nosotros.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin Alkawari.” Wani miktam ta Dawuda. Don koyarwa. Sa’ad da ya yaƙi Aram-Naharayim da Aram-Zoba, da kuma sa’ad da Yowab ya dawo ya bugi mutanen Edom dubu goma sha biyu a Kwarin Gishiri. Ka ki mu, ya Allah, ka kuma fashe kāriyarmu; ka yi fushi da mu, yanzu ka mai da mu!
2 Hiciste temblar la tierra, abrístela; sana sus quebraduras, porque titubea.
Ka girgiza ƙasar ka kuma tsaga ta; ka daure karayarta, gama tana rawa.
3 Hiciste ver a tu pueblo duras cosas: hicístenos beber vino de temblor.
Ka nuna wa mutanenka lokutan wahala; ka ba mu ruwan inabin da ya sa muka bugu.
4 Has dado a los que te temen una bandera que alcen por amor de la verdad. (Selah)
Amma ga waɗanda suke tsoronka, ka ɗaga tuta don a buɗe gāba da baka. (Sela)
5 Para que se escapen tus amados: salva con tu diestra, y óyeme.
Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
6 Dios habló en su santidad: Yo me alegraré: partiré a Siquem, y mediré al valle de Socot.
Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Da nasara zan rarraba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
7 Mío es Galaad, y mío es Manasés: y Efraím es la fortaleza de mi cabeza; Judá mi legislador;
Gileyad nawa ne, Manasse kuma nawa ne; Efraim shi ne hular kwanona, Yahuda kuma sandar mulkina.
8 Moab, la olla de mi lavatorio: sobre Edom echaré mi zapato; sobre mí triunfa, o! Palestina.
Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirarin nasara.”
9 ¿Quién me llevará a la ciudad fortalecida? ¿quién me llevará hasta Idumea?
Wa zai kawo ni birnin katanga? Wa zai bishe ni zuwa Edom?
10 Ciertamente tú, o! Dios, que nos habías desechado; y no salías, o! Dios, con nuestros ejércitos.
Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
11 Dános socorro contra el enemigo, que vana es la salud de los hombres.
Ka ba mu gudummawa a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
12 En Dios haremos proezas; y él pisará nuestros enemigos.
Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattake abokan gābanmu.

< Salmos 60 >