< Salmos 30 >
1 Ensalzarte he, o! Jehová, porque me has ensalzado: y no hiciste alegrar a mis enemigos de mí.
Zabura ce. Wata waƙa. Don keɓewar haikali. Ta Dawuda. Zan girmama ka Ya Ubangiji, gama ka tsamo ni daga zurfafa ba ka bar abokan gābana sun yi farin ciki a kaina ba.
2 Jehová, Dios mío, clamé a ti, y me sanaste.
Ya Ubangiji Allahna, na yi kira gare ka don taimako ka kuwa warkar da ni.
3 Jehová, hiciste subir del sepulcro mi alma: dísteme vida de mi descendimiento a la sepultura. (Sheol )
Ya Ubangiji, ka dawo da ni daga kabari; ka kiyaye ni daga gangarawa zuwa cikin rami. (Sheol )
4 Cantád a Jehová sus misericordiosos: y celebrad la memoria de su santidad.
Ku rera ga Ubangiji, ku tsarkakansa; ku yabi sunansa mai tsarki.
5 Porque un momento hay en su furor, mas vida en su voluntad: a la tarde reposará el lloro, y a la mañana vendrá la alegría.
Gama fushinsa na ɗan lokaci ne amma alherinsa har matuƙa ne; mai yiwuwa a yi kuka da dare amma farin ciki kan zo da safe.
6 Y yo dije en mi quietud: No resbalaré jamás.
Sa’ad da nake lafiya, na ce, “Ba zan jijjigu ba.”
7 Porque tú, Jehová, por tu benevolencia asentaste mi monte con fortaleza: mas escondiste tu rostro, y yo fui conturbado.
Ya Ubangiji, sa’ad da ka yi mini alheri, ka sa katangar dutsena ya tsaya daram; amma sa’ad da ka ɓoye fuskarka, sai in cika da tsoro.
8 A ti, o! Jehová, llamaré: y al Señor suplicaré.
A gare ka, ya Ubangiji, na yi kira; a gare ka Ubangiji na yi kukan neman jinƙai.
9 ¿Qué provecho hay en mi muerte, cuando yo descendiere al hoyo? ¿Loarte ha el polvo? ¿anunciará tu verdad?
“Wace riba ce a hallakata, a kuma gangarawa ta zuwa cikin rami? Ƙura za tă yabe ka ne? Za tă iya yin shelar amincinka?
10 Oye, o! Jehová, y ten misericordia de mí: Jehová, sé mi ayudador.
Ka ji, ya Ubangiji, ka kuwa yi mini jinƙai; Ya Ubangiji, ka zama taimakona.”
11 Tú tornaste mi endecha en baile: desataste mi saco, y ceñísteme de alegría.
Ka mai da kukata ta zama rawa; ka tuɓe rigar makokina ka sa mini na farin ciki,
12 Por tanto a ti canté gloria, y no callé: Jehová Dios mío, para siempre te alabaré.
don zuciyata za tă iya rera gare ka ba kuwa za tă yi shiru ba. Ya Ubangiji Allahna, zan yi maka godiya har abada.