< Salmos 29 >

1 Dad a Jehová, o! hijos de fuertes, dad a Jehová la gloria y la fortaleza.
Zabura ta Dawuda. Ku ba da girma ga Ubangiji, ya ku manya, ku ba da girma ga Ubangiji saboda ɗaukaka da kuma ƙarfinsa.
2 Dad a Jehová la gloria de su nombre: humilláos a Jehová en el glorioso santuario.
Ku ba da girma ga Ubangiji, ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku bauta wa Ubangiji cikin ɗaukakar tsarkinsa.
3 Voz de Jehová sobre las aguas: el Dios de gloria hizo tronar: Jehová, sobre las muchas aguas.
Muryar Ubangiji tana a bisa ruwaye; Allah Maɗaukaki ya yi tsawa, Ubangiji ya yi tsawa a bisa manyan ruwaye.
4 Voz de Jehová con potencia: voz de Jehová con gloria.
Muryar Ubangiji mai iko ce; muryar Ubangiji da girma take.
5 Voz de Jehová que quebranta los cedros; y quebrantó Jehová los cedros del Líbano.
Muryar Ubangiji ta kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon. Ubangiji ya kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon kucu-kucu.
6 E hízolos saltar como los becerros: al Líbano, y al Sirión como hijos de unicornios.
Ya sa dutsen Lebanon ya yi ta tsalle kamar ɗan maraƙi, Siriyon kuma kamar ɗan jakin jeji.
7 Voz de Jehová que corta llamas de fuego.
Muryar Ubangiji ta buga da walƙatar walƙiya.
8 Voz de Jehová que hará temblar al desierto: hará temblar Jehová al desierto de Cádes.
Muryar Ubangiji ta girgiza hamada Ubangiji ya girgiza Hamadan Kadesh.
9 Voz de Jehová que hará estar de parto a las ciervas, y desnudará a las breñas: y en su templo todos los suyos le dicen gloria.
Muryar Ubangiji ta murɗa itatuwan oak ya kakkaɓe itatuwan kurmi. Kuma a cikin haikalinsa kowa ya ce, “Ɗaukaka!”
10 Jehová estuvo en el diluvio, y asentóse Jehová por rey para siempre.
Ubangiji na zaune yana sarauta a bisa rigyawa; Ubangiji yana sarauta kamar Sarki har abada.
11 Jehová dará fortaleza a su pueblo: Jehová bendecirá a su pueblo en paz.
Ubangiji kan ba da ƙarfi ga mutanensa; Ubangiji kan albarkace mutanensa da salama.

< Salmos 29 >