< Salmos 126 >
1 Cuando Jehová hiciere tornar los cautivos de Sión, seremos como los que sueñan.
Waƙar haurawa. Sa’ad da Ubangiji ya dawo da kamammu zuwa Sihiyona, mun kasance kamar mutanen da suka yi mafarki.
2 Entonces nuestra boca se henchirá de risa, y nuestra lengua de alabanza: entonces dirán entre los Gentiles: Grandes cosas ha hecho Jehová con estos.
Bakunanmu sun cika da dariya, harsunanmu da waƙoƙin farin ciki. Sai ana faɗi a cikin al’ummai, “Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominsu.”
3 Grandes cosas ha hecho Jehová con nosotros: seremos alegres.
Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominmu, mun kuwa cika da farin ciki.
4 Haz volver, o! Jehová, nuestros cautivos, como los arroyos en el austro.
Ka maido da wadatarmu, ya Ubangiji kamar rafuffuka a Negeb.
5 Los que sembraron con lágrimas, con regocijos segarán.
Waɗanda suka yi shuka da hawaye za su yi girbi da waƙoƙin farin ciki.
6 Irá yendo y llorando el que lleva la preciosa simiente: mas viniendo, vendrá con regocijo trayendo sus gavillas.
Shi da ya fita yana kuka, riƙe da iri don shuki, zai dawo da waƙoƙin farin ciki, ɗauke da dammuna.