< Salmos 119 >
1 Bienaventurados los perfectos de camino: los que andan en la ley de Jehová.
Albarka ta tabbata ga waɗanda rayuwarsu ba ta da abin zargi, waɗanda suke tafiya bisa ga dokar Ubangiji.
2 Bienaventurados los que guardan sus testimonios; y con todo el corazón le buscan.
Albarka ta tabbata ga waɗanda suke kiyaye ƙa’idodinsa suke kuma nemansa da dukan zuciyarsu.
3 Ítem, los que no hacen iniquidad, andan en sus caminos.
Ba sa yin wani abin da ba daidai ba; suna tafiya a hanyoyinsa.
4 Tú encargaste tus mandamientos, que sean muy guardados.
Ka shimfiɗa farillan da dole a yi biyayya da su.
5 ¡Ojalá fuesen ordenados mis caminos a guardar tus estatutos!
Kash, da a ce hanyoyina tsayayyu ne a yin biyayya da ƙa’idodinka mana!
6 Entonces no sería yo avergonzado, cuando mirase en todos tus mandamientos.
Da ba zan sha kunya ba sa’ad da na lura da dukan umarnanka.
7 Alabarte he con rectitud de corazón, cuando aprendiere los juicios de tu justicia.
Zan yabe ka da zuciya ta gaskiya yayinda nake koyon dokokinka masu adalci.
8 Tus estatutos guardaré: no me dejes enteramente.
Zan yi biyayya da ƙa’idodinka; kada ka yashe ni ɗungum.
9 ¿Con qué limpiará el mozo su camino? cuando guardare tu palabra.
Yaya matashi zai kiyaye hanyarsa da tsabta? Sai ta yin rayuwa bisa ga maganarka.
10 Con todo mi corazón te he buscado: no me dejes errar de tus mandamientos.
Na neme ka da dukan zuciyata; kada ka bar ni in kauce daga umarnanka.
11 En mi corazón he guardado tus dichos, para no pecar contra ti.
Na ɓoye maganarka a cikin zuciyata don kada in yi maka zunubi.
12 Bendito tú, o! Jehová, enséñame tus estatutos.
Yabo ya tabbata gare ka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
13 Con mis labios he contado todos los juicios de tu boca.
Da leɓunana na ba da labarin dukan dokokin da suka fito bakinka.
14 En el camino de tus testimonios me he regocijado, como sobre toda riqueza.
Na yi farin ciki da bin farillanka yadda mutum yakan yi farin ciki da arziki mai yawa.
15 En tus mandamientos meditaré; y consideraré tus caminos.
Na yi tunani a kan farillanka na kuma lura da hanyoyinka.
16 En tus estatutos me recrearé: no me olvidaré de tus palabras.
Na yi murna a cikin ƙa’idodinka; ba zan ƙyale maganarka ba.
17 Haz este bien a tu siervo; que viva, y guarde tu palabra.
Ka yi alheri ga bawanka, zan kuwa rayu; zan yi biyayya da maganarka.
18 Destapa mis ojos; y miraré las maravillas de tu ley.
Ka buɗe idanuna don in iya gani abubuwan banmamaki a cikin dokarka.
19 Advenedizo soy yo en la tierra: no encubras de mi tus mandamientos.
Ni baƙo ne a duniya; kada ka ɓoye mini umarnanka.
20 Quebrantada está mi alma de desear tus juicios todo el tiempo.
Zuciyata ta ƙosa saboda marmari don dokokinka koyaushe.
21 Destruiste a los soberbios malditos, que yerran de tus mandamientos.
Ka tsawata wa masu fariya, waɗanda suke la’anta waɗanda kuma suka kauce daga umarnanka.
22 Aparta de mí oprobio y menosprecio; porque tus testimonios he guardado.
Ka cire mini ba’a da reni, gama ina kiyaye farillanka.
23 Príncipes también se asentaron, y hablaron contra mí: meditando tu siervo en tus estatutos.
Ko da yake masu mulki sun zauna tare suna ɓata mini suna, bawanka zai yi tunani a kan ƙa’idodinka.
24 También tus testimonios son mis delicias: los varones de mi consejo.
Farillanka ne abin farin cikina; su ne mashawartana.
25 Apegóse con el polvo mi alma: vivifícame según tu palabra.
An kwantar da ni ƙasa cikin ƙura; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
26 Mis caminos te conté, y respondísteme: enséñame tus estatutos.
Na ba da labari hanyoyina ka kuma amsa mini; ka koya mini ƙa’idodinka.
27 El camino de tus mandamientos házme entender; y meditaré en tus maravillas.
Bari in gane koyarwar farillanka; sa’an nan zan yi tunani a kan abubuwan banmamakinka.
28 Mi alma se destila de ansia: confírmame según tu palabra.
Raina ya gaji da baƙin ciki; ka ƙarfafa ni bisa ga maganarka.
29 Camino de mentira aparta de mí: y de tu ley házme misericordia.
Ka kiyaye ni daga hanyoyin ruɗu; ka yi mini alheri ta wurin dokokinka.
30 El camino de la verdad escogí: tus juicios he puesto delante de mí.
Na zaɓi hanyar gaskiya; na sa zuciyata a kan dokokinka.
31 Allegádome he a tus testimonios, o! Jehová, no me avergüences.
Na riƙe farillanka kankan, ya Ubangiji; kada ka sa in sha kunya.
32 Por el camino de tus mandamientos correré: cuando ensanchares mi corazón.
Ina gudu a kan hanyar umarnanka, gama ka’yantar da zuciyata.
33 Enséñame, o! Jehová, el camino de tus estatutos; y guardarle he hasta el fin.
Ka koya mini Ya Ubangiji, don in bi ƙa’idodinka; sa’an nan zan kiyaye su har ƙarshe.
34 Dáme entendimiento, y guardaré tu ley; y guardarla he de todo corazón.
Ka ba ni ganewa, zan kuwa kiyaye dokarka in kuma yi biyayya da ita da dukan zuciyata.
35 Guíame por la senda de tus mandamientos; porque en ella tengo mi verdad.
Ka bi da ni a hanyar umarnanka, gama a can zan sami farin ciki.
36 Inclina mi corazón a tus testimonios: y no a avaricia.
Ka juye zuciyata wajen farillanka ba wajen riba ta sonkai ba.
37 Aparta mis ojos, que no vean la vanidad: avívame en tu camino.
Ka juye idanuna daga abubuwa marasa amfani; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
38 Confirma tu palabra a tu siervo, que te teme.
Ka cika alkawarinka ga bawanka, saboda a ji tsoronka.
39 Quita de mí el oprobio que he temido; porque buenos son tus juicios.
Ka kawar da shan kunyar da nake tsoro, gama dokokinka nagari ne.
40 He aquí yo he codiciado tus mandamientos: en tu justicia avívame.
Ina marmarin farillanka ƙwarai! Ka kiyaye raina cikin adalcinka.
41 Y véngame tu misericordia, o! Jehová: tu salud, conforme a tu dicho.
Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zo gare ni, ya Ubangiji, cetonka bisa ga alkawarinka;
42 Y daré por respuesta a mi avergonzador, que en tu palabra he confiado.
sa’an nan zan amsa wa masu cin mutuncina, gama na dogara ga maganarka.
43 Y no quites de mi boca palabra de verdad en ningún tiempo; porque a tu juicio espero.
Kada ka ƙwace maganarka daga bakina, gama na sa zuciyata a dokokinka.
44 Y guardaré tu ley siempre, por siglo y siglo.
Kullayaumi zan yi biyayya da dokokinka, har abada abadin.
45 Y andaré en anchura, porque busqué tus mandamientos.
Zan yi ta yawo a sake gama na nemi farillanka.
46 Y hablaré de tus testimonios delante de los reyes; y no me avergonzaré.
Zan yi maganar farillanka a gaban sarakuna ba kuwa za a kunyata ni ba,
47 Y deleitarme he en tus mandamientos, que amé.
gama ina farin ciki da umarnanka saboda ina ƙaunarsu.
48 Y alzaré mis manos a tus mandamientos, que amé; y meditaré en tus estatutos.
Na ɗaga hannuwana ga umarnanka, waɗanda nake ƙauna, ina kuma tunani a kan ƙa’idodinka.
49 Acuérdate de la palabra dada a tu siervo: en la cual me has hecho esperar.
Tuna da maganarka ga bawanka, gama ka ba ni bege.
50 Esta es mi consolación en mi aflicción; porque tu dicho me vivificó.
Ta’aziyyata cikin wahalata ita ce alkawarinka yana kiyaye raina.
51 Los soberbios se burlaron mucho de mí: de tu ley no me he apartado.
Masu fariya suna yi mini ba’a ba tare da an hana su ba, amma ban rabu da dokar ba.
52 Acordéme, o! Jehová, de tus juicios antiguos, y me consolé.
Na tuna da dokokinka na tun dā, ya Ubangiji, na kuwa sami ta’aziyya a cikinsu.
53 Temblor me tomó a causa de los impíos, que dejan tu ley.
Fushi ya kama ni saboda mugaye, waɗanda suka keta dokokinka.
54 Canciones me son tus estatutos en la casa de mis peregrinaciones.
Ƙa’idodinka su ne kan waƙata a duk inda na sauka.
55 Acordéme en la noche de tu nombre, o! Jehová, y guardé tu ley.
Da dare na tuna da sunanka, ya Ubangiji, zan kuwa kiyaye dokarka.
56 Esto tuve, porque guardaba tus mandamientos.
Wannan shi ne na saba yi, ina yin biyayya da farillanka.
57 Mi porción, o! Jehová, dije, será guardar tus palabras.
Kai ne rabona, ya Ubangiji; na yi alkawarin in kiyaye maganarka.
58 En tu presencia supliqué de todo corazón: ten misericordia de mí según tu dicho.
Na nemi fuskarka da dukan zuciyata; ka yi mini alheri bisa ga alkawarinka.
59 Consideré mis caminos, y torné mis pies a tus testimonios.
Na lura da hanyoyina na kuma mayar da matakaina ga farillanka.
60 Apresuréme, y no me detuve, a guardar tus mandamientos.
Zan gaggauta ba zan ɓata lokaci ba in yi biyayya da umarnanka.
61 Compañías de impíos me han saqueado: mas no me he olvidado de tu ley.
Ko da yake mugaye sun ɗaura ni da igiyoyi, ba zan manta da dokokinka ba.
62 A media noche me levantaré a alabarte sobre los juicios de tu justicia.
Da tsakar dare nakan tashi in gode maka saboda dokokinka masu adalci.
63 Compañero soy yo a todos los que te temieren; y guardaren tus mandamientos.
Ni aboki ne ga duk mai tsoronka, ga duk wanda yake bin farillanka.
64 De tu misericordia, o! Jehová, está llena la tierra: tus estatutos enséñame.
Duniya ta cika da ƙaunarka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
65 Bien has hecho con tu siervo, o! Jehová, conforme a tu palabra.
Ka yi wa bawanka alheri bisa ga maganarka, ya Ubangiji.
66 Bondad de sentido, y sabiduría enséñame, porque a tus mandamientos he creído.
Ka koya mini sani da kuma hukunci mai kyau, gama na gaskata a umarnanka.
67 Antes que fuera humillado, yo erraba: mas ahora tu palabra guardo.
Kafin in sha wahala na kauce, amma yanzu ina biyayya da maganarka.
68 Bueno eres tú, y bienhechor: enséñame tus estatutos.
Kai nagari ne, kuma abin da kake yi yana da kyau; ka koya mini ƙa’idodinka.
69 Compusieron sobre mí mentira los soberbios: mas yo de todo corazón guardaré tus mandamientos.
Ko da yake masu fariya sun shafe ni da ƙarairayi, na kiyaye farillanka da dukan zuciyata.
70 Engrosóse su corazón como sebo: mas yo en tu ley me he deleitado.
Zukatansu sun yi tauri da kuma marasa tausayi amma ina farin ciki a dokarka.
71 Bueno me es haber sido humillado, para que aprenda tus estatutos.
Ya yi kyau da na sha wahala don in koyi ƙa’idodinka.
72 Mejor me es la ley de tu boca, que millares de oro y de plata.
Doka daga bakinka ya fi mini daraja fiye da azurfa da zinariya guda dubu.
73 Tus manos me hicieron, y me compusieron: házme entender, y aprenderé tus mandamientos.
Hannuwanka ne suka yi suka kuma siffanta ni; ka ba ni ganewa don in koyi umarnanka.
74 Los que te temen, me verán, y se alegrarán; porque a tu palabra he esperado.
Bari waɗanda suke tsoronka su yi farin ciki sa’ad da suke gan ni, gama na sa zuciyata a maganarka.
75 Conozco, o! Jehová, que tus juicios son justicia, y que con verdad me afligiste.
Ya Ubangiji na sani, cewa dokokinka masu adalci ne, kuma cikin aminci ka hore ni.
76 Sea ahora tu misericordia para consolarme, conforme a lo que has dicho a tu siervo.
Bari ƙaunarka marar ƙarewa tă yi mini ta’aziyya, bisa ga alkawarinka ga bawanka.
77 Vénganme tus misericordias, y viva; porque tu ley es mis delicias.
Bari tausayinka yă zo mini don in rayu, gama dokarka ce farin cikina.
78 Sean avergonzados los soberbios, porque sin causa me han calumniado: yo empero meditaré en tus mandamientos.
Bari masu girman kai su sha kunya saboda abubuwa marasa kyau da suke yi mini ba dalili; amma zan yi tunani a kan farillanka.
79 Tórnense a mí los que te temen, y saben tus testimonios.
Bari waɗanda suke tsoronka su juya gare ni, waɗanda suka gane da farillanka.
80 Sea mi corazón perfecto en tus estatutos; porque no sea avergonzado.
Bari zuciyata ta kasance marar abin zargi wajen ƙa’idodinka, don kada in sha kunya.
81 Desfalleció de deseo mi alma por tu salud, esperando a tu palabra.
Raina ya tafke da marmari don cetonka, amma na sa zuciyata a maganarka.
82 Desfallecieron mis ojos por tu dicho, diciendo: ¿Cuándo me consolarás?
Idanuna sun gaji, suna jiran alkawarinka; Na ce, “Yaushe za ka ta’azantar da ni?”
83 Porque estoy como el odre al humo: mas no he olvidado tus estatutos.
Ko da yake ni kamar salkar ruwan inabi ne a cikin hayaƙi, ban manta da ƙa’idodinka ba.
84 ¿Cuántos son los días de tu siervo? ¿cuándo harás juicio contra los que me persiguen?
Har yaushe bawanka zai yi ta jira? Yaushe za ka hukunta masu tsananta mini?
85 Los soberbios me han cavado hoyos: mas no según tu ley.
Masu girman kai sun haƙa mini rami, sun ƙetare dokarka.
86 Todos tus mandamientos son verdad, sin causa me persiguen, ayúdame.
Dukan umarnanka abin dogara ne; ka taimake ni, gama mutane suna tsananta mini ba dalili.
87 Casi me han consumido por tierra: mas yo no he dejado tus mandamientos.
Sun kusa gama da ni a duniya, amma ban bar bin farillanka ba.
88 Conforme a tu misericordia vivifícame; y guardaré los testimonios de tu boca.
Ka kiyaye raina bisa ga ƙaunarka, zan kuwa yi biyayya da farillan bakinka.
89 Para siempre, o! Jehová, permanece tu palabra en los cielos.
Maganarka, ya Ubangiji madawwamiya ce; tana nan daram a cikin sammai.
90 Por generación y generación es tu verdad: tú afirmaste la tierra, y persevera.
Amincinka yana cin gaba cikin dukan zamanai; ka kafa duniya ta kuma dawwama.
91 Por tu ordenación perseveran hasta hoy; porque todas ellas son tus siervos.
Dokokinka sun dawwama har yă zuwa yau, gama dukan abubuwa suna maka hidima.
92 Si tu ley no hubiese sido mis delicias, ya hubiera perecido en mi aflicción.
Da ba don dokarka ce farin cikina ba, da na hallaka a cikin azabana.
93 Nunca jamás me olvidaré de tus mandamientos; porque con ellos me has vivificado.
Ba zan taɓa manta da farillanka ba, gama ta wurinsu ne ka kiyaye raina.
94 Tuyo soy yo, guárdame; porque tus mandamientos he buscado.
Ka cece ni, gama ni naka ne; na yi ƙoƙarin neman farillanka.
95 Los impíos me han aguardado para destruirme: mas yo entenderé en tus testimonios.
Mugaye suna jira su hallaka ni, amma zan yi ta tunani a kan farillanka.
96 A toda perfección he visto fin: ancho es tu mandamiento en gran manera.
Ga duk cikakke na ga kāsawa; amma umarnanka ba su da iyaka.
97 ¡Cuánto he amado tu ley! todo el día ella es mi meditación.
Kash, ga yadda nake ƙaunar dokarka! Ina tunani a kanta dukan yini.
98 Más que mis enemigos me has hecho sabio con tus mandamientos; porque me son eternos.
Umarnanka suna sa in zama mai hikima fiye da abokan gābana, gama kullum suna tare da ni.
99 Más que todos mis enseñadores he entendido; porque tus testimonios han sido mi meditación.
Ina da ganewa sosai fiye da dukan malamaina, gama ina tunani a kan farillanka.
100 Más que los viejos he entendido: porque he guardado tus mandamientos.
Ina da ganewa fiye da dattawa, gama ina biyayya da farillanka.
101 De todo mal camino detuve mis pies, para guardar tu palabra.
Na kiyaye ƙafafuna daga kowace muguwar hanya domin in yi biyayya da maganarka.
102 De tus juicios no me aparté; porque tú me enseñaste.
Ban rabu da dokokinka ba, gama kai da kanka ne ka koya mini.
103 ¡Cuán dulces han sido a mi paladar tus palabras! más que la miel a mi boca.
Ɗanɗanon maganarka akwai zaki, sun ma fi zuma zaki a bakina!
104 De tus mandamientos, he adquirido entendimiento; por tanto he aborrecido todo camino de mentira.
Na sami ganewa daga farillanka; saboda haka ina ƙin kowace hanyar da ba daidai ba.
105 Lámpara es a mis pies tu palabra, y lumbre a mi camino.
Maganarka fitila ce ga ƙafafuna haske kuma a kan hanyata.
106 Juré, y afirmé, de guardar los juicios de tu justicia.
Na yi rantsuwa na kuma tabbatar da shi, cewa zan bi dokokinka masu adalci.
107 Afligido estoy en gran manera, o! Jehová: vivifícame conforme a tu palabra.
Na sha wahala sosai; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga maganarka.
108 Los sacrificios voluntarios de mi boca, ruégote, o! Jehová, que te sean agradables; y enséñame tus juicios.
Ka karɓi yabon bakina da nake yi da yardar rai, ya Ubangiji, ka kuwa koya mini dokokinka.
109 Mi alma está en mi palma de continuo: mas de tu ley no me he olvidado.
Ko da yake kullum ina riƙe da raina a hannuwana, ba zan manta da dokarka ba.
110 Los impíos me pusieron lazo: empero yo no me desvié de tus mandamientos.
Mugaye sun kafa mini tarko, amma ban kauce daga farillanka ba.
111 Por heredad he tomado tus testimonios para siempre; porque son el gozo de mi corazón.
Farillanka su ne gādona har abada; su ne farin cikin zuciyata.
112 Mi corazón incliné a hacer tus estatutos de continuo hasta el fin.
Zuciyata ta shirya a kan kiyaye ƙa’idodinka har ƙarshe.
113 Las cautelas aborrezco, y tu ley he amado.
Na ƙi mutane masu baki biyu, amma ina ƙauna dokarka.
114 Mi escondedero y mi escudo eres tú, a tu palabra he esperado.
Kai ne mafakata da garkuwata; na sa zuciyata a maganarka.
115 Apartáos de mí los malignos, y guardaré los mandamientos de mi Dios.
Ku rabu da ni, ku masu aikata mugunta, don in kiyaye umarnan Allahna!
116 Susténtame conforme a tu palabra, y viviré, y no me avergüences de mi esperanza.
Ka raya ni bisa ga alkawarinka, zan kuwa rayu; kada ka bari a gwale sa zuciyata.
117 Sosténme, y seré salvo; y deleitarme he en tus estatutos siempre.
Ka riƙe ni za a kuma cece ni; kullayaumi zan ɗauka ƙa’idodinka da muhimmanci.
118 Tú atropellaste a todos los que yerran de tus estatutos; porque mentira es su engaño.
Ka ki dukan waɗanda suka kauce daga ƙa’idodinka, gama yaudararsu banza ne.
119 Como escorias hiciste deshacer a todos los impíos de la tierra: por tanto yo he amado tus testimonios.
Dukan mugayen duniya ka zubar kamar datti; saboda haka nake ƙaunar farillanka.
120 Mi carne se ha erizado de temor de ti; y de tus juicios he tenido miedo.
Naman jikina na rawan jiki don tsoronka; na cika da tsoron dokokinka.
121 Juicio y justicia he hecho: no me dejes a mis opresores.
Na aikata abin da yake mai adalci da kuma daidai; kada ka ni a hannun masu danne ni.
122 Responde por tu siervo para bien: no me hagan violencia los soberbios.
Ka tabbatar da lafiyar bawanka; kada ka bar masu girman kai su danne ni.
123 Mis ojos desfallecieron por tu salud, y por el dicho de tu justicia.
Idanuna sun gaji, da jiran cetonka, da jiran alkawarinka mai adalci.
124 Haz con tu siervo según tu misericordia; y enséñame tus estatutos.
Ka yi da bawanka bisa ga ƙaunarka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
125 Tu siervo soy yo; dáme entendimiento, para que sepa tus testimonios.
Ni bawanka ne, ka ba ni fahimi don in gane farillanka.
126 Tiempo es de hacer, o! Jehová: disipado han tu ley.
Lokaci ya yi da za ka yi wani abu, ya Ubangiji; ana karya dokarka.
127 Por tanto yo he amado tus mandamientos más que el oro, y más que el oro muy puro.
Saboda ina ƙaunar umarnanka fiye da zinariya, kai, fiye da zinariya zalla,
128 Por tanto todos los mandamientos de todas las cosas estimé rectos: todo camino de mentira aborrecí.
saboda kuma ina lura da dukan farillanka da kyau, na ƙi kowace hanyar da ba daidai ba.
129 Maravillosos son tus testimonios; por tanto los ha guardado mi alma.
Farillanka masu banmamaki ne; saboda haka nake yin biyayya da su.
130 El principio de tus palabras alumbra: hace entender a los simples.
Fassarar maganganunka sukan ba da haske; sukan ba da ganewa ga marar ilimi.
131 Mi boca abrí y suspiré; porque deseaba tus mandamientos.
Ina hakkin da bakina a buɗe, ina marmarin umarnanka.
132 Mira a mí, y ten misericordia de mí: como acostumbras con los que aman tu nombre.
Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, yadda kullum ka yi wa waɗanda suke ƙaunar sunanka.
133 Ordena mis pasos con tu palabra; y ninguna iniquidad se enseñoree de mí.
Ka bi da sawuna bisa ga maganarka; kada ka bar zunubi yă mallake ni.
134 Redímeme de la violencia de los hombres; y guardaré tus mandamientos.
Ka fanshe ni daga mutane masu danniya, don in yi biyayya da farillanka.
135 Haz que tu rostro resplandezca sobre tu siervo; y enséñame tus estatutos.
Ka sa fuskarka ta haskaka a kan bawanka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
136 Ríos de aguas descendieron de mis ojos; porque no guardaban tu ley.
Hawaye suna malalowa daga idanuna kamar rafi, gama ba a biyayya da dokarka.
137 Justo eres tú, o! Jehová, y rectos tus juicios.
Mai adalci ne kai, ya Ubangiji, dokokinka kuma daidai ne.
138 Encargáste la justicia, es a saber, tus testimonios, y tu verdad.
Farillan da ka shimfiɗa masu adalci ne; su kuma abin dogara ne ƙwarai.
139 Mi zelo me ha consumido; porque mis enemigos se olvidaron de tus palabras.
Kishina ya cinye ni ɗungum, gama abokan gābana sun yi biris da maganganunka.
140 Afinada es tu palabra en gran manera; y tu siervo la ama.
An gwada alkawuranka sarai, bawanka kuwa yana ƙaunarsu.
141 Pequeño soy yo y desechado: mas no me he olvidado de tus mandamientos.
Ko da yake ni ba kome ba ne an kuwa rena ni, ba na manta da farillanka.
142 Tu justicia es justicia eterna; y tu ley verdad.
Adalcinka dawwammame ne dokar kuma gaskiya ce.
143 Aflicción y angustia me hallaron: mas tus mandamientos fueron mis delicias.
Wahala da damuwa suna a kaina, amma umarnanka su ne farin cikina.
144 Justicia eterna son tus testimonios: dáme entendimiento, y viviré.
Farillanka daidai ne har abada; ka ba ni ganewa don in rayu.
145 Clamé con todo mi corazón: respóndeme Jehová, y guardaré tus estatutos.
Na yi kira da dukan zuciyata; ka amsa mini, ya Ubangiji, zan kuwa yi biyayya da ƙa’idodinka.
146 Clamé a ti; sálvame, y guardaré tus testimonios.
Na yi kira gare ka; ka cece ni zan kuwa kiyaye farillanka.
147 Previne al alba y clamé, esperé tu palabra.
Na tashi kafin fitowar rana na kuma yi kukan neman taimako; na sa zuciyata a maganarka.
148 Previnieron mis ojos las veladas, para meditar en tus palabras.
Ban rufe idanuna ba dukan dare, don in yi tunani a kan alkawuranka.
149 Oye mi voz conforme a tu misericordia, o! Jehová: vivifícame conforme a tu juicio.
Ka ji muryata bisa ga ƙaunarka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga dokokinka.
150 Acercáronse los que me persiguen a la maldad: alejáronse de tu ley.
Waɗanda suke ƙirƙiro mugayen dabaru suna nan kusa, amma suna nesa da dokarka.
151 Cercano estás tú, Jehová, y todos tus mandamientos son verdad.
Duk da haka kana kusa, ya Ubangiji, kuma dukan umarnanka gaskiya ne.
152 Ya ha mucho que he entendido de tus mandamientos, que para siempre los fundaste.
Tun tuni na koyi daga farillanka cewa ka kafa su su kasance har abada.
153 Mira mi aflicción, y escápame; porque de tu ley no me he olvidado,
Ka dubi wahalata ka cece ni, gama ban manta da dokarka ba.
154 Pleitea mi pleito, y redímeme: vivifícame con tu palabra.
Ka kāre manufata ka kuma fanshe ni, ka cece rai na kamar yadda ka alkawarta!
155 Lejos está de los impíos la salud; porque no buscan tus estatutos.
Ceto yana nesa da mugaye, gama ba sa neman ƙa’idodinka.
156 Muchas son tus misericordias, o! Jehová: vivifícame conforme a tus juicios.
Tausayinka da girma yake, ya Ubangiji; ka kiyaye raina bisa ga dokokinka.
157 Muchos son mis persiguidores y mis enemigos; mas de tus testimonios no me he apartado.
Maƙiya masu yawa ne suke tsananta mini, amma ban rabu da farillanka ba.
158 Veía a los prevaricadores, y carcomíame; porque no guardaban tus palabras.
Na dubi marasa aminci da ƙyama, gama ba sa yin biyayya da maganarka.
159 Mira, o! Jehová, que amo tus mandamientos: vivifícame conforme a tu misericordia.
Dubi yadda nake ƙaunar farillanka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga ƙaunarka.
160 El principio de tu palabra es verdad; y eterno todo juicio de tu justicia.
Dukan maganganunka gaskiya ne; dukan dokokinka masu adalci madawwami ne.
161 Príncipes me han perseguido sin causa: mas de tus palabras tuvo miedo mi corazón.
Masu mulki suna tsananta mini ba dalili, amma zuciyata na rawan jiki game da maganarka.
162 Regocíjome yo sobre tu palabra, como el que halla muchos despojos.
Ina farin ciki da alkawarinka kamar yadda wani kan sami ganima mai girma.
163 La mentira aborrezco, y abomino; tu ley amo.
Na ƙi ina kuma ƙyamar ƙarya amma ina ƙaunar dokarka.
164 Siete veces al día te alabo sobre los juicios de tu justicia.
Sau bakwai a rana ina yabonka saboda dokokinka masu adalci.
165 Mucha paz tienen los que aman tu ley; y no hay para ellos tropezón.
Waɗanda suke ƙaunar dokarka suna da babban salama, kuma babu abin da zai sa su yi tuntuɓe.
166 Tu salud he esperado, o! Jehová; y tus mandamientos he practicado.
Ina jiran cetonka, ya Ubangiji, ina kuma bin umarnanka.
167 Mi alma ha guardado tus testimonios; y en gran manera los he amado.
Ina biyayya da farillanka, gama ina ƙaunarsu ƙwarai.
168 Guardado he tus mandamientos, y tus testimonios; porque todos mis caminos están delante de ti.
Ina biyayya da farillanka da kuma koyarwarka, gama dukan hanyoyina sanannu ne gare ka.
169 Acérquese mi clamor delante de ti, o! Jehová: dáme entendimiento conforme a tu palabra.
Bari kukata ta zo gare ka, ya Ubangiji; ka ba ni ganewa bisa ga maganarka.
170 Venga mi oración delante de ti: escápame conforme a tu dicho.
Bari roƙona yă zo gabanka; ka cece ni bisa ga alkawarinka.
171 Mis labios rebosarán alabanza, cuando me enseñares tus estatutos.
Bari leɓunana su cika da yabonka, gama ka koya mini ƙa’idodinka.
172 Hablará mi lengua tus palabras; porque todos tus mandamientos son justicia.
Bari harshena yă rera game da maganarka, gama dukan umarnanka masu adalci ne.
173 Sea tu mano en mi socorro; porque tus mandamientos he escogido.
Bari hannunka yă kasance a shirye don yă taimake ni, gama na zaɓi farillanka.
174 Deseado he tu salud, o! Jehová; y tu ley es mis delicias.
Ina marmarin cetonka, ya Ubangiji, dokarka kuwa ita ce farin cikina.
175 Viva mi alma, y alábete; y tus juicios me ayuden.
Bari in rayu don in yabe ka, bari kuma dokokinka su raya ni.
176 Yo me perdí, como oveja que se pierde: busca a tu siervo, porque no me he olvidado de tus mandamientos.
Na kauce kamar ɓatacciyar tunkiya. Ka nemi bawanka, gama ban manta da umarnanka ba.