< Salmos 116 >
1 Amé a Jehová, porque ha oído mi voz: mis ruegos.
Ina ƙaunar Ubangiji, gama ya ji muryata; ya ji kukata ta neman jinƙai.
2 Porque ha inclinado su oído a mí; y en mis días le llamaré,
Domin ya juye kunnensa gare ni, zan kira gare shi muddin ina da rai.
3 Rodeáronme los dolores de la muerte, las angustias del sepulcro me hallaron: angustia y dolor había hallado: (Sheol )
Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni, wahalar kabari sun zo a kaina; na cika da wahala da ɓacin rai. (Sheol )
4 Y llamé el nombre de Jehová: Escapa ahora mi alma, o! Jehová.
Sai na kira ga sunan Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!”
5 Clemente es Jehová y justo, y misericordioso nuestro Dios.
Ubangiji mai alheri ne da kuma mai adalci; Allahnmu yana cike da tausayi.
6 Guarda a los sencillos Jehová: yo estaba debilitado y salvóme.
Ubangiji yana tsare masu tawali’u; sa’ad da nake cikin tsananin bukata, ya cece ni.
7 Vuelve, o! alma mía, a tu reposo; porque Jehová te ha hecho bien.
Ka kwantar da hankali, ya raina, gama Ubangiji mai alheri ne a gare ka.
8 Porque has librado mi alma de la muerte, mis ojos de las lágrimas, mis pies del rempujón.
Gama kai, ya Ubangiji, ka ceci raina daga mutuwa, idanuna daga hawaye, ƙafafuna daga tuntuɓe,
9 Andaré delante de Jehová en las tierras de los vivos.
don in iya tafiya a gaban Ubangiji a ƙasar masu rai.
10 Creí, por tanto hablé: y fui afligido en gran manera.
Na gaskata, saboda haka na ce, “An azabtar da ni ƙwarai.”
11 Y dije en mi apresuramiento: Todo hombre es mentiroso.
Kuma cikin rikicewana na ce, “Dukan mutane maƙaryata ne.”
12 ¿Qué pagaré a Jehová por todos sus beneficios sobre mí?
Yaya zan sāka wa Ubangiji saboda dukan alherinsa gare ni?
13 El vaso de saludes tomaré; e invocaré el nombre de Jehová.
Zan daga kwaf na ceto in kuma kira ga sunan Ubangiji.
14 Ahora pagaré mis votos a Jehová delante de todo su pueblo.
Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa.
15 Estimada es en los ojos de Jehová la muerte de sus piadosos.
Abu mai daraja a gaban Ubangiji shi ne mutuwar tsarkakansa.
16 Así es, o! Jehová; porque yo soy tu siervo, yo soy tu siervo, hijo de tu sierva, tú rompiste mis prisiones.
Ya Ubangiji, da gaske ni bawanka ne; ni bawanka ne, ɗan baiwarka; ka’yantar da ni daga sarƙoƙi.
17 A ti sacrificaré sacrificio de alabanza; y el nombre de Jehová invocaré.
Zan yi hadayar godiya gare ka in kuma kira bisa sunan Ubangiji.
18 Ahora pagaré mis votos a Jehová delante de todo su pueblo;
Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa,
19 En los patios de la casa de Jehová; en medio de ti, o! Jerusalem. Alelu- Jah.
a filayen gidan Ubangiji, a tsakiyarki, ya Urushalima. Yabi Ubangiji.