< Salmos 107 >

1 Alabád a Jehová, porque es bueno; porque para siempre es su misericordia.
Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 Dígan lo los redimidos de Jehová, los que ha redimido de poder del enemigo,
Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
3 Y los ha congregado de las tierras, del oriente y del occidente, del aquilón y de la mar.
su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
4 Anduvieron perdidos por el desierto, por la soledad sin camino: no hallando ciudad de población.
Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
5 Hambrientos, y sedientos: su alma desfallecía en ellos.
Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
6 Y clamaron a Jehová en su angustia; y escapólos de sus aflicciones.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
7 Y encaminólos en camino derecho; para que viniesen a ciudad de población.
Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
8 Alaben pues ellos la misericordia de Jehová, y sus maravillas con los hijos de los hombres.
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
9 Porque hartó al alma menesterosa; y al alma hambrienta hinchió de bien.
gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
10 Los que moraban en tinieblas, y sombra de muerte, aprisionados en aflicción, y en hierros;
Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
11 Por cuanto fueron rebeldes a las palabras de Jehová; y aborrecieron el consejo del Altísimo:
gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
12 Y él quebrantó con trabajo sus corazones: cayeron, y no hubo quien les ayudase:
Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
13 Y clamaron a Jehová en su angustia: escapólos de sus aflicciones.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
14 Sacólos de las tinieblas, y de la sombra de muerte; y rompió sus prisiones.
Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
15 Alaben pues ellos la misericordia de Jehová, y sus maravillas con los hijos de los hombres.
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
16 Porque quebrantó las puertas de acero; y desmenuzó los cerrojos de hierro.
gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
17 Insensatos, a causa del camino de su rebelión; y a causa de sus maldades fueron afligidos.
Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
18 Su alma abominó toda vianda; y llegaron hasta las puertas de la muerte.
Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
19 Y clamaron a Jehová en su angustia; y salvólos de sus aflicciones.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
20 Envió su palabra, y curólos; y escapólos de sus sepulturas.
Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
21 Alaben pues ellos la misericordia de Jehová; y sus maravillas con los hijos de los hombres.
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
22 Y sacrifiquen sacrificios de alabanza; y enarren sus obras con jubilación.
Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
23 Los que descendieron a la mar en navíos: y contratan en las muchas aguas;
Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
24 Ellos han visto las obras de Jehová, y sus maravillas en el mar profundo.
Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
25 El dijo, y salió el viento de la tempestad, que levanta sus ondas:
Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
26 Suben a los cielos, descienden a los abismos: sus almas se derriten con el mal.
Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
27 Tiemblan, y titubean como borrachos; y toda su ciencia es perdida.
Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
28 Y claman a Jehová en su angustia; y escápalos de sus aflicciones.
Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
29 Hace parar la tempestad en silencio; y callan sus ondas.
Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
30 Y alégranse, porque se reposaron; y guíalos al puerto que quieren.
Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
31 Alaben pues ellos la misericordia de Jehová, y sus maravillas con los hijos de los hombres.
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
32 Y ensálcenle en congregación de pueblo; y en consistorio de ancianos le loen.
Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
33 Vuelve los ríos en desierto; y los manaderos de las aguas en sed:
Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
34 La tierra fructífera en salados; por la maldad de los que la habitan.
ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
35 Vuelve el desierto en estanques de aguas, y la tierra seca en manaderos de aguas:
Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
36 Y aposenta allí hambrientos; y aderezan allí ciudad de población:
a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
37 Y siembran campos, y plantan viñas; y hacen fruto de renta:
Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
38 Y bendícelos, y se multiplican en gran manera: y no disminuye sus bestias.
ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
39 Y después son menoscabados, y abatidos de tiranía, de males, y de congojas.
Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
40 El derrama menosprecio sobre los príncipes: y les hace andar errantes, vagabundos, sin camino.
shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
41 Y levanta al pobre de la pobreza; y vuelve las familias como ovejas.
Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
42 Vean los rectos, y alégrense; y toda maldad cierre su boca.
Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
43 ¿Quién es sabio, y guardará estas cosas; y entenderá las misericordias de Jehová?
Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.

< Salmos 107 >