< Job 33 >
1 Por tanto oye ahora, Job, mis razones, y escucha todas mis palabras.
“Amma yanzu, Ayuba, ka saurari abin da zan ce; ka sa hankali ga kowane abin da zan faɗa.
2 He aquí, ahora yo abriré mi boca, y mi lengua hablará en mi garganta.
Zan yi magana; kalmomina suna dab da fitowa daga bakina.
3 Mis razones declararán la rectitud de mi corazón, y mis labios hablarán pura sabiduría.
Abin da zan faɗa gaskiya ne daga cikin zuciyata; bakina zai faɗi gaskiyar abin da na sani.
4 El Espíritu de Dios me hizo, y la inspiración del Omnipotente me dio vida.
Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
5 Si pudieres, respóndeme: dispón, está delante de mí.
Ka amsa mini in za ka iya; ka yi shirin fuskanta ta.
6 Heme aquí a mí en lugar de Dios, conforme a tu dicho: de lodo soy yo también formado.
Ni kamar ka nake a gaban Allah; ni ma daga ƙasa aka yi ni.
7 He aquí que mi terror no te espantará, ni mi mano se agravará sobre ti.
Kada ka ji tsorona, ba abin da zai fi ƙarfinka.
8 De cierto tú dijiste a mis oídos, y yo oí la voz de tus palabras:
“Amma ka faɗa na ji, na ji daidai abin da ka faɗa,
9 Yo soy limpio, y sin rebelión: yo soy inocente, y no hay maldad en mí;
‘ni mai tsarki ne marar zunubi; ina da tsabta kuma ba ni da laifi.
10 He aquí que él buscó achaques contra mí, y me tiene por su enemigo;
Duk da haka Allah ya same ni da laifi; ya ɗauke ni maƙiyinsa,
11 Puso mis pies en el cepo, y guardó todas mis sendas.
ya daure ƙafafuna da sarƙa; yana tsaron duk inda na bi.’
12 He aquí en esto no has hablado justamente: responderte he, que mayor es Dios que el hombre.
“Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
13 ¿Por qué tomaste pleito contra él? porque él no dirá todas sus palabras.
Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?
14 Antes en una o en dos maneras hablará Dios al que no ve.
Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
15 Por sueño de visión nocturna, cuando el sueño cae sobre los hombres, cuando se adormecen sobre el lecho;
A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
16 Entonces revela al oído de los hombres; y les señala su castigo;
mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
17 Para quitar al hombre de la mala obra, y apartar del varón la soberbia.
don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
18 Así detendrá su alma de corrupción, y su vida de ser pasada a cuchillo.
don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
19 También sobre su cama es castigado con dolor fuertemente, en todos sus huesos:
“Ko kuma mutum yă sha horo ta wurin kwanciya da ciwo da rashin jin daɗi cikin ƙasusuwansa,
20 Que le hace que su vida aborrezca el pan, y su alma la comida suave.
yadda zai ji ƙyamar abinci, har yă ƙi son abinci mafi daɗi.
21 Su carne desfallece sin verse; y sus huesos, que antes no se veían, serán levantados.
Naman jikinsa ya lalace ba wani abu mai kyau a ciki kuma ƙasusuwansa da suke a rufe da tsoka yanzu duk sun fito.
22 Y su alma se acercará del sepulcro, y su vida, de los matadores.
Ransa yana matsawa kusa da rami, ransa kuma kusa da’yan aikan mutuwa.
23 Si hubiere cerca de él algún elocuente anunciador muy escogido, que anuncie al hombre su justicia,
Duk da haka, in akwai mala’ika a gefensa kamar matsakanci, ɗaya daga cikin dubu, da zai gaya wa mutum abin da yake daidai gare shi,
24 Que le diga: que Dios tuvo misericordia de él, que le libró de descender al sepulcro, que halló redención.
yă yi masa alheri yă ce, ‘Kada ka bari yă fāɗa cikin rami, na samu fansa dominsa.’
25 Su carne se enternecerá más que de un niño, y volverá a los días de su mocedad.
Sa’an nan fatar jikinsa za tă zama sabuwa kamar ta jariri; za tă zama kamar lokacin da yake matashi.
26 Orará a Dios, y amarle ha; y verá su faz con júbilo: y él dará al hombre el pago de su justicia.
Ya yi addu’a ga Allah ya kuwa samu alheri a wurinsa, yana ganin fuskar Allah yana kuma yin sowa don murna; Allah ya mayar da shi ya zama mai adalci.
27 Él mira sobre los hombres; y el que dijere: Pequé, y pervertí lo recto, y no me ha aprovechado:
Sa’an nan sai ya zo wurin, wurin mutane ya ce, ‘Na yi zunubi, na kauce wa abin da yake daidai, amma ban samu abin da ya kamata in samu ba.
28 Dios redimirá su alma, que no pase al sepulcro, y su vida se verá en luz.
Ya fanshi raina daga fāɗawa cikin rami, kuma zan rayu in ji daɗin hasken.’
29 He aquí, todas estas cosas hace Dios dos, tres veces con el hombre.
“Allah ya yi wa mutum duk waɗannan, sau biyu, har ma sau uku.
30 Para apartar su alma del sepulcro, y para ilustrarle con la luz de los vivientes.
Ya juyo da ransa daga fāɗawa cikin rami, don hasken rai ya haskaka a kansa.
31 Escucha, Job, y óyeme: calla, y yo hablaré:
“Ka sa hankali da kyau, Ayuba, ka saurare ni; ka yi shiru zan yi magana.
32 Y si hubiere palabras, respóndeme: habla, porque yo te quiero justificar.
In kana da abin da za ka ce, ka amsa mini; yi magana, domin ina so in’yantar da kai.
33 Y si no, óyeme tú a mí: calla, y enseñarte he sabiduría.
Amma in ba haka ba, sai ka saurare ni; yi shiru, zan kuma koya maka hikima.”