< Job 30 >

1 Mas ahora los más mozos de días que yo, se rien de mí, cuyos padres yo desdeñara de ponerlos con los perros de mi ganado,
“Amma yanzu suna yi mini ba’a waɗanda na girme su, waɗanda iyayensu maza ba su isa su zama karnukan kiwon garken tumakina ba.
2 Porque ¿para qué había yo menester la fuerza de sus manos, en los cuales pereció el tiempo?
Ina amfani ƙarfin hannuwansu gare ni, tun da ba su da sauran kuzari?
3 Por causa de la pobreza y de la hambre solos: que huían a la soledad, al lugar tenebroso, asolado y desierto.
Duk sun rame don rashi da yunwa, suna yawo a gaigayar ƙasa a kufai da dare.
4 Que cogían malvas entre los árboles, y raíces de enebros para calentarse.
A cikin jeji suna tsinkar ganyaye marasa daɗi, jijiyoyin itacen kwakwa ne abincinsu.
5 Eran echados de entre las gentes, y todos les daban grita como a ladrón.
An kore su daga cikin mutanensu, aka yi musu ihu kamar ɓarayi.
6 Que habitaban en las barrancas de los arroyos, en las cavernas de la tierra, y en las piedras.
An sa dole su zauna a kwazazzabai da kuma cikin kogunan duwatsu da kuma cikin ramummuka cikin ƙasa.
7 Que bramaban entre las matas, y se congregaban debajo de las espinas.
Suka yi ta kuka kamar dabbobi a jeji, suka taru a ƙarƙashin sarƙaƙƙiya.
8 Hijos de viles, y hombres sin nombre: mas bajos que la misma tierra.
Mutane marasa hankali marasa suna, an kore su daga ƙasar.
9 Y ahora yo soy su canción, y soy hecho a ellos refrán.
“Yanzu kuma’ya’yansu maza su suke yi mini ba’a cikin waƙa na zama abin banza a gare su.
10 Abomínanme, aléjanse de mí; y aun de mi rostro no detuvieron su saliva.
Suna ƙyamata suna guduna; suna tofa mini miyau a fuska.
11 Porque Dios desató mi cuerda, y me afligió; y quitaron el freno delante de mi rostro.
Yanzu da Allah ya kunce bakana ya ba ni wahala sun raba ni da mutuncina.
12 A la mano derecha se levantaron los muchachos; rempujaron mis pies, y pisaron sobre mí las sendas de su contrición.
A hannun damana’yan tā-da-na-zaune-tsaye sun tayar; sun sa tarko a ƙafafuna, sun yi shirin hallaka ni.
13 Mi senda derribaron: aprovecháronse de mi quebrantamiento; contra los cuales no hubo ayudador.
Sun ɓata mini hanyata; sun yi nasara cikin hallaka ni, ba tare da wani ya taimake su ba.
14 Vinieron como por portillo ancho: revolviéronse por mi calamidad.
Suka nufo ni daga kowane gefe; suka auko mini da dukan ƙarfinsu.
15 Turbaciones se convirtieron sobre mí: combatieron como un viento mi voluntad, y mi salud como nube que pasa.
Tsoro ya rufe ni; an kawar mini mutuncina kamar da iska, dukiyata ta watse kamar girgije.
16 Y ahora mi alma está derramada en mí: días de aflicción me han comprendido.
“Yanzu raina yana ƙarewa; kwanakin wahala sun kama ni.
17 De noche taladra sobre mí mis huesos, y mis pulsos no reposan.
Dare ya huda ƙasusuwana; ina ta shan azaba ba hutawa.
18 Con la grandeza de la fuerza del dolor mi vestidura es mudada; cíñeme como el collar de mi ropa.
A cikin girman ikonsa Allah ya zama kamar riga a jikina; ya shaƙe ni kamar wuyan rigata.
19 Derribóme en el lodo, y soy semejante al polvo, y a la ceniza.
Ya jefa ni cikin laka, na zama ba kome ba sai ƙura da toka.
20 Clamo a ti, y no me oyes: me presento, y no me echas de ver.
“Na yi kuka gare ka ya Allah, amma ba ka amsa mini ba. Na tashi tsaye, amma sai ka dube ni kawai.
21 Háste tornado cruel para mí: con la fortaleza de tu mano me amenazas.
Ka dube ni ba tausayi; Ka kai mini hari da ƙarfin hannunka.
22 Levantásteme, e hicísteme cabalgar sobre el viento, y derretiste en mí el ser.
Ka ɗaga ni sama ka ɗora ni a kan iska; ka jujjuya ni cikin hadari.
23 Porque yo conozco que me tornas a la muerte, y a la casa determinada a todo viviente.
Na san za ka sauko da ni ga mutuwa zuwa wurin da kowane mai rai zai je.
24 Mas él no extenderá la mano contra el sepulcro; ¿clamarán los sepultados cuando él los quebrantare?
“Ba shakka ba mai ɗora hannu a kan mutumin da yake cikin wahala. Lokacin da ya yi kukan neman taimako a cikin wahalarsa.
25 ¿No lloré yo al afligido, y mi alma no se entristeció sobre el menesteroso?
Ashe ban yi kuka domin waɗanda suke cikin damuwa ba? Ko zuciyata ba tă yi baƙin ciki domin matalauta ba?
26 Cuando esperaba el bien, entonces me vino el mal; y cuando esperaba la luz, vino la oscuridad.
Duk da haka sa’ad da nake begen abu mai kyau, mugun abu ne ya zo; Sa’ad da nake neman haske, sai duhu ya zo.
27 Mis entrañas hierven, y no reposan: previniéronme días de aflicción.
Zuciyata ba tă daina ƙuna ba; ina fuskantar kwanakin wahala.
28 Denegrido anduve, y no por el sol: levantéme en la congregación, y clamé.
Na yi baƙi ƙirin, amma ba rana ce ta ƙona ni ba. Na tsaya a cikin mutane, na kuma yi kuka don taimako.
29 Hermano fui de los dragones, y compañero de las hijas del avestruz.
Na zama ɗan’uwan diloli, na zama abokan mujiyoyi.
30 Mi cuero está denegrido sobre mí, y mis huesos se secaron con sequedad.
Fatar jikina ta yi baƙi tana ɓarewa; jikina yana ƙuna da zazzaɓi.
31 Y mi arpa se tornó en luto, y mi órgano en voz de lamentantes.
Garayata ta zama ta makoki, sarewata kuma ta zama ta kuka.

< Job 30 >