< Job 3 >

1 Después de esto abrió Job su boca, y maldijo su día.
Bayan wannan Ayuba ya buɗe baki ya la’anta ranar da aka haife shi.
2 Y exclamó Job, y dijo:
Ayuba ya ce,
3 Perezca el día en que yo fui nacido, y la noche que dijo: Concebido es varón.
“A hallaka ranar da aka haife ni, da kuma daren da aka ce, ‘An haifi jariri namiji!’
4 Aquel día fuera tinieblas, y Dios no curara de él desde arriba, ni claridad resplandeciera sobre él.
Bari ranan nan ta zama duhu; kada Allah yă kula da ita; kada rana tă yi haske a wannan rana.
5 Ensuciáranle tinieblas y sombra de muerte; reposara sobre él nublado, que le hiciera horrible como día caluroso.
Bari duhu da inuwa mai duhu ta sāke rufe ta; gizagizai kuma su rufe ta; duhu kuma ya rufe haskenta.
6 A aquella noche ocupara oscuridad, ni fuera contada entre los días del año, ni viniera en el número de los meses.
Bari duhu mai yawa yă rufe daren nan; kada a haɗa ta cikin kwanakin shekara, ko kuma cikin kwanakin watanni.
7 Oh si fuera aquella noche solitaria, que no viniera en ella canción;
Bari daren yă zama marar amfani; kada a ji wata sowa ta farin ciki.
8 Maldijéranla los que maldicen al día, los que se aparejan para levantar su llanto.
Bari waɗanda suke la’anta ranaku su la’anta wannan rana su waɗanda suke umartar dodon ruwa.
9 Las estrellas de su alba fueran oscurecidas; esperara la luz, y no viniera; ni viera los párpados de la mañana.
Bari taurarinta na safe su zama duhu; bari ranar tă yi ta jiran ganin haske amma kada tă gani,
10 Porque no cerró las puertas del vientre donde yo estaba, ni escondió de mis ojos la miseria.
gama ba tă hana uwata ɗaukar cikina, don ta hana ni shan wahalan nan ba.
11 ¿Por qué no morí yo desde la matriz, y fui traspasado en saliendo del vientre?
“Me ya sa ban mutu ba da za a haife ni, ko kuma in mutu sa’ad da ana haihuwata ba?
12 ¿Por qué me previnieron las rodillas, y para qué los pechos que mamase?
Me ya sa aka haife ni, aka tanada nono na sha na rayu?
13 Porque ahora yaciera y reposara; durmiera, y entonces tuviera reposo,
Da yanzu ina kwance cikin salama; da ina barcina cikin salama
14 Con los reyes, y con los consejeros de la tierra, que edifican para sí los desiertos;
tare da sarakuna da mashawarta a cikin ƙasa, waɗanda suka gina wa kansu wuraren da yanzu duk sun rushe,
15 O con los príncipes que poseen el oro, que hinchen sus casas de plata.
da shugabanni waɗanda suke da zinariya, waɗanda suka cika gidajensu da azurfa.
16 O ¿ por qué no fui escondido como abortivo, como los pequeñitos que nunca vieron luz?
Ko kuma don me ba a ɓoye ni a cikin ƙasa kamar jaririn da aka haifa ba rai ba, kamar jaririn da bai taɓa ganin hasken rana ba.
17 Allí los impíos dejaron el miedo, y allí descansaron los de cansadas fuerzas.
A wurin mugaye za su daina yin mugunta, gajiyayyu kuma za su huta.
18 Allí también reposaron los cautivos, no oyeron la voz del exactor.
Waɗanda aka daure za su sami jin daɗin; an sake su ba za su sāke jin ana tsawata masu ba.
19 Allí está el chico y el grande: allí es el siervo libre de su señor.
Manyan da ƙanana suna a can, bawa kuma ya sami’yanci daga wurin maigidansa.
20 ¿Por qué dio luz al trabajado, y vida a los amargos de ánimo?
“Don me ake ba da haske ga waɗanda suke cikin ƙunci, rai kuma ga masu ɗacin rai
21 Que esperan la muerte, y no la hay: y la buscan más que tesoros.
ga waɗanda suke neman mutuwa amma ba su samu ba, waɗanda suke nemanta kamar wani abu mai daraja a ɓoye,
22 Que se alegran de grande alegría, y se gozan cuando hallan el sepulcro.
waɗanda suke farin ciki sa’ad da suka kai kabari?
23 Al hombre que no sabe por donde vaya, y que Dios le encerró.
Don me aka ba mutum rai, mutumin da bai san wani abu game da kansa ba, mutumin da Allah ya kange shi.
24 Porque antes que mi pan, viene mi suspiro: y mis gemidos corren como aguas.
Baƙin ciki ya ishe ni maimakon abinci; ina ta yin nishi ba fasawa;
25 Porque el temor que me espantaba, me ha venido, y háme acontecido lo que temía.
Abin da nake tsoro ya faru da ni; abin da ba na so ya same ni.
26 Nunca tuve paz, nunca me sosegué, ni nunca me reposé; y vínome turbación.
Ba ni da salama, ba natsuwa; ba ni da hutu, sai wahala kawai.”

< Job 3 >