< Job 17 >
1 Mi huelgo es corrompido, mis días son cortados, y el sepulcro me está aparejado.
Na karaya, kwanakina sun kusa ƙarewa, kabari yana jirana.
2 Ya no hay conmigo sino escarnecedores, en cuyas amarguras se detienen mis ojos.
Ba shakka masu yi mini ba’a suna kewaye da ni; idanuna suna ganin tsokanar da suke yi mini.
3 Pon ahora, y dáme fianzas contigo: ¿quién tocará ahora mi mano?
“Ya Allah, ka ba ni abin da ka yi mini alkawari. Wane ne zai kāre ni?
4 Porque el corazón de ellos has escondido de entendimiento: por tanto no los ensalzarás.
Ka rufe zuciyarsu yadda ba za su iya ganewa ba, saboda haka ba za ka bari su yi nasara ba.
5 El que denuncia lisonjas a sus prójimos, los ojos de sus hijos desfallezcan.
In mutum ya juya wa abokansa baya don a ba shi wata lada’ya’yansa za su makance.
6 El me ha puesto por parábola de pueblos, y delante de ellos he sido tamboril.
“Allah ya sa na zama abin da kowa yake magana a kai wanda kowa yake tofa wa miyau a fuska.
7 Y mis ojos se oscurecieron de desabrimiento, y todos mis pensamientos han sido como sombra.
Idanuna ba sa gani sosai don baƙin ciki; jikina ya zama kamar inuwa kawai
8 Los rectos se maravillarán de esto, y el inocente se despertará contra el hipócrita.
Mutanen da suke masu adalci wannan abu ya ba su tsoro; marasa laifi sun tayar wa marasa tsoron Allah.
9 Mas el justo retendrá su carrera; y el limpio de manos aumentará la fuerza.
Duk da haka, masu adalci za su ci gaba da tafiya a kan hanyarsu, waɗanda hannuwansu suke da tsabta kuma za su ƙara ƙarfi.
10 Mas volvéd todos vosotros, y veníd ahora, y no hallaré entre vosotros sabio.
“Amma ku zo dukanku, ku sāke gwadawa! Ba zan sami mutum ɗaya mai hikima ba a cikinku.
11 Mis días se pasaron, y mis pensamientos fueron arrancados, los pensamientos de mi corazón.
Kwanakina sun wuce, shirye-shiryena sun ɓaci haka kuma abubuwan da zuciyata take so.
12 Pusiéron me la noche por día, y la luz cercana delante de las tinieblas.
Mutanen nan sun juya rana ta zama dare. A tsakiyar duhu suka ce, ‘Haske yana kusa.’
13 Si yo espero, el sepulcro es mi casa: en las tinieblas hice mi cama. (Sheol )
In kabari ne begen da nake da shi kaɗai, in na shimfiɗa gadona a cikin duhu, (Sheol )
14 A la huesa dije: Mi padre eres tú: a los gusanos: Mi madre, y mi hermano.
In na ce wa kabari, ‘Kai ne mahaifina,’ tsutsa kuma ke ce, ‘Mahaifiyata’ ko ‘’yar’uwata,’
15 ¿Dónde pues estará ahora mi esperanza? y mi esperanza, ¿quién la verá?
To, ina begena yake? Wane ne zai iya ganin wani bege domina?
16 A los rincones de la huesa descenderán; y juntamente descansarán en el polvo. (Sheol )
Ko begena zai tafi tare da ni zuwa kabari ne? Ko tare za a bizne mu cikin ƙura?” (Sheol )