< Romanos 11 >

1 Pregunto: ¿Dios desechó a su pueblo? ¡Claro que no! También yo soy israelita, de [la] descendencia de Abraham, de [la ]tribu de Benjamín.
To, ina da tambaya. Allah ya ƙi mutanensa ne? Sam, ko kaɗan! Ni mutumin Isra’ila ne kaina, zuriyar Ibrahim kuwa, daga kabilar Benyamin.
2 Dios no desechó a su pueblo, al cual conoció con anticipación. ¿No supieron lo que dice la Escritura en cuanto a Elías, cómo invoca a Dios contra Israel?
Allah bai ƙi mutanensa da ya rigya sani ba. Ba ku san abin da Nassi ya faɗa game da Iliya ba, yadda ya kawo kuka ga Allah a kan Isra’ila ya ce,
3 Señor, mataron a tus profetas y destruyeron tus altares. Yo quedé solo, y buscan mi vida.
“Ya Ubangiji, sun karkashe annabawanka suka kuma rurrushe bagadanka; ni kaɗai na ragu, suna kuma neman raina”?
4 ¿Pero qué le dice la respuesta divina? Me reservé a 7.000 varones, quienes no doblaron rodilla ante baal.
Wace amsa ce Allah ya ba shi? “Na keɓe wa kaina dubu bakwai waɗanda ba su yi wa Ba’al sujada ba.”
5 Así también en el tiempo presente quedó un remanente escogido por gracia.
Haka ma, a wannan zamani akwai ragowar da aka zaɓa ta wurin alheri.
6 Si es por gracia, ya no es por obras. De otra manera, la gracia ya no es gracia.
In kuwa na alheri ne, ba sauran cewa ya dogara ga ayyuka ke nan. In ba haka ba, ashe, alheri ba alheri ba ne kuma.
7 Entonces ¿qué diremos? Lo que Israel buscaba no [lo] obtuvo, pero los elegidos [lo] obtuvieron y los demás fueron endurecidos.
To, sai me? Abin da Isra’ila suka nema da himma ba su samu ba, amma zaɓaɓɓun suka samu. Sauran suka taurare,
8 Como está escrito: Dios les dio espíritu de adormecimiento, ojos para no ver y oídos para no oír hasta el día de hoy.
kamar yadda yake a rubuce cewa, “Allah ya ba su ruhun ruɗewa, idanu don su kāsa gani, da kuma kunnuwa don su kāsa ji, har yă zuwa yau.”
9 David dice: Que su banquete se convierta en engaño y en trampa, Y en piedra de tropiezo y en pago para ellos.
Dawuda kuma ya ce, “Bari teburin cin abincinsu yă zama musu tarko, sanadin fāɗuwa da dutsen sa tuntuɓe da kuma ramuwa a kansu.
10 Que se oscurezcan sus ojos para que no vean, Y doble la espalda de ellos para siempre.
Bari idanunsu su duhunta don kada su iya gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.”
11 Pregunto: ¿Tropezaron para que cayeran? ¡Claro que no! Pero con su transgresión [vino] la salvación a los gentiles para provocarlos a celos.
Har yanzu ina da tambaya. Sun yi tuntuɓe har ya kai ga fāɗuwar da ba za su iya tashi ba ne? Sam, ko kaɗan! A maimako, saboda laifinsu ne ceto ya zo ga Al’ummai don a sa mutanen Isra’ila su ji kishi.
12 Si su transgresión es riqueza del mundo, y su derrota, riqueza de los gentiles, ¡cuánto más su plena restauración!
Amma in laifinsu yana nufin albarka ga duniya, hasararsu kuma albarka ga Al’ummai, ina misalin yalwar da albarkunsu za su kawo!
13 Pero hablo a ustedes los gentiles por cuanto yo soy apóstol de los gentiles. Honro mi ministerio para ver
Ina magana da ku ne fa Al’ummai. Tun da yake ni manzo ne ga Al’ummai, ina taƙama da aikin nan nawa,
14 si de alguna manera provoco a celos a mis parientes y logro la salvación de algunos de ellos.
da fata zan rura kabilata a ta kowace hanya su ji kishi har ma yă sa in ceci waɗansunsu.
15 Porque si la reprobación de ellos es reconciliación del mundo, ¿qué será su aceptación? Solo vida de entre [los] muertos.
Gama in ƙinsu da aka yi ya zama sulhu ga duniya, me karɓarsu za tă zama in ba rai daga matattu ba?
16 Si lo primero de la masa es santo, también la masa. Si la raíz es santa, también las ramas.
In sashen da aka miƙa a matsayin nunan fari tsattsarka ne, to, sauran ma tsattsarka ne; in saiwar tsattsarka ce, to, sauran rassan ma tsattsarka ne.
17 Pero si algunas de las ramas fueron desgajadas, y tú, que eras un olivo silvestre, fuiste injertado entre ellas y participaste de la rica savia de la raíz del olivo,
In an sassare waɗansu rassa, kai kuwa da kake kai zaitun jeji, aka ɗauke ka aka kuma yi muku aure, a yanzu kuwa kana shan ni’imar saiwar zaitun ɗin nan tare da sauran rassan,
18 no te enaltezcas contra las ramas. Si te enalteces, recuerda que no sustentas a la raíz, sino la raíz a ti.
kada ka yi taƙama cewa ka fi waɗancan rassan da aka sassare. In kuwa ka yi haka, to, ka yi la’akari da wannan. Ba kai ne kake taimakon saiwar ba, saiwar ce take taimakonka.
19 Entonces dirás: Unas ramas fueron desgajadas para que yo fuera injertado.
To, kana iya cewa, “An sassare rassan ne don a ɗaura aure da ni.”
20 Tienes razón. Fueron desgajadas por incredulidad, y tú por la fe estás firme. No seas arrogante, sino teme.
Haka yake. Amma an sassare su ne saboda rashin bangaskiya, kai kuma kana tsaye ta wurin bangaskiya. Kada ka yi taƙama, sai dai ka ji tsoro.
21 Porque si Dios no preservó las ramas naturales, tampoco te preservará.
Gama in har Allah bai bar rassan nan na asali ba, kai ma ba zai bar ka ba.
22 Considera, pues, [la ]bondad y [la ]severidad de Dios para los que cayeron, pero bondad para ti, si permaneces en la bondad. De otra manera tú también serás cortado.
Ka lura fa da alheri da kuma tsananin Allah, tsanani ga waɗanda suka fāɗi, amma alheri a gare ka, da fata za ka ci gaba cikin alherinsa. In ba haka ba, kai ma za a sare ka.
23 Aun ellos, si dejan la incredulidad, serán injertados, porque Dios es poderoso para volverlos a injertar.
In kuwa ba su nace cikin rashin bangaskiya ba, za a sāke ɗaura aure da su, domin Allah yana iya sāke haɗa su.
24 Porque si tú fuiste cortado de un olivo silvestre natural, y contra naturaleza fuiste injertado en un olivo cultivado, ¿cuánto más estas ramas naturales serán injertadas en el propio olivo?
Kai ma da aka saro daga zaitun ɗin da asalinsa yake na jeji, aka ɗaura aure da kai a jikin zaitun ɗin na gida, saɓanin yadda aka saba, balle waɗannan rassa na asali, da za a ɗaura aure da su a jikin zaitun ɗin nan nasu na asali?
25 Hermanos, para que no presuman de sabios, quiero que sepan este misterio: que a Israel en parte le ocurrió un endurecimiento hasta que entre la plenitud de los gentiles.
Ba na so ku kasance cikin rashin sani game da wannan asirin’yan’uwa, domin kada ku ɗaga kai. Isra’ila sun ɗanɗana sashe na taurarewa har sai da shigowar Al’ummai masu yawa ya cika.
26 Así todo Israel será rescatado, como está escrito: El Libertador vendrá de Sion, y quitará la impiedad de Jacob.
Ta haka kuwa za a ceci dukan Isra’ila, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Mai ceto zai zo daga Sihiyona; zai kawar da rashin bin Allah daga Yaƙub.
27 Y éste será mi Pacto con ellos cuando [les] quite sus pecados.
Wannan kuwa shi ne alkawarina da su sa’ad da na ɗauke musu zunubansu.”
28 Ciertamente, en cuanto a las Buenas Noticias, [los judíos] son enemigos por causa de ustedes, pero en cuanto a la elección, son muy amados por Dios por causa de los antepasados.
Game da zancen nan na bishara kuwa, su abokan gāba ne saboda ku; amma game da zaɓen kuwa, su ƙaunatattunsa ne, albarkacin kakannin kakanninsu,
29 Porque los dones y el llamamiento de Dios son irrevocables.
gama kyautar Allah da kiransa ba a sokewa.
30 Pues así como en otro tiempo ustedes fueron desobedientes a Dios, pero por la desobediencia de ellos, ahora se [les] concedió misericordia,
Kamar yadda a dā can ku da kuke marasa biyayya ga Allah kuka sami jinƙai yanzu ta dalilin rashin biyayyarsu,
31 así también ahora éstos fueron desobedientes, para que por la misericordia que ustedes recibieron, ellos también logren misericordia.
haka su ma suka zama marasa biyayya a yanzu domin su ma su sami jinƙai ta dalilin jinƙan da Allah ya yi muku.
32 Porque Dios encerró a todos en desobediencia para tener misericordia de todos. (eleēsē g1653)
Gama Allah ya daure dukan mutane ga rashin biyayya don yă nuna jinƙai ga kowa. (eleēsē g1653)
33 ¡Oh profundidad de [la ]riqueza, de [la ]sabiduría y del conocimiento de Dios! ¡Cuán inalcanzables son sus juicios e inescrutables sus caminos!
Kai, zurfin yalwar hikima da kuma sanin Allah yana nan a yalwace! Hukunce-hukuncensa kuma su fi gaban bincike, hanyoyinsa kuwa sun wuce gaban ganewa!
34 Porque ¿quién entendió [la] mente del Señor? ¿O quién fue su consejero?
“Wa ya taɓa sanin zuciyar Ubangiji? Ko kuwa yă ba shi shawara?”
35 ¿O quién le dio por adelantado para que Él le devuelva?
“Wa ya taɓa ba wa Allah wani abu, da Allah zai sāka masa?”
36 Porque de Él, por medio de Él y en Él son todas las cosas. ¡A Él sea la gloria por los siglos! Amén. (aiōn g165)
Gama daga gare shi, ta wurinsa, da kuma saboda shi ne dukan abubuwa suka kasance. Ɗaukaka ta tabbata a gare shi har abada! Amin. (aiōn g165)

< Romanos 11 >