< Salmos 92 >

1 Bueno es alabar a Yavé Y cantar salmos a tu Nombre, oh ʼElyón.
Zabura ce. Waƙa ce. Domin ranar Asabbaci. Yana da kyau a yabi Ubangiji a kuma yi kiɗi ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka,
2 Anunciar por la mañana tu misericordia Y tu fidelidad cada noche
don a yi shelar ƙaunarka da safe amincinka kuma da dare,
3 Con el decacordio y el salterio, Con el armonioso tono del arpa.
da kiɗin molo mai tsirkiya goma da kuma ƙarar garaya.
4 Porque Tú, oh Yavé, me alegraste con lo que hiciste. Por las obras de tus manos doy gritos de júbilo.
Gama ka sa na yi murna ta wurin ayyukanka, ya Ubangiji; na rera don farin ciki saboda ayyukan hannuwanka.
5 ¡Cuán grandes son tus obras, oh Yavé! Tus pensamientos son muy profundos.
Ina misalin ayyukanka, ya Ubangiji, tunaninka da zurfi suke ƙwarai!
6 El hombre necio no sabe Y el insensato no entiende esto:
Mutum marar azanci ba zai sani ba, wawa ba zai gane ba,
7 Que cuando los perversos brotan como hierba, Y florecen todos los que hacen iniquidad, [Solo sucede] para que sean destruidos eternamente.
cewa ko da yake mugaye suna girma kamar ciyawa kuma dukan masu aikata mugunta suna haɓaka, za a hallaka su har abada.
8 Pero Tú, oh Yavé, eres altísimo para siempre.
Amma kai, ya Ubangiji, za a ɗaukaka har abada.
9 Porque ya veo que tus enemigos, oh Yavé, Ya veo que tus enemigos perecen. Son dispersados todos los obradores de iniquidad.
Gama tabbatacce abokan gābanka, ya Ubangiji, tabbatacce abokan gābanka za su hallaka; za a watsar da dukan masu aikata mugunta.
10 Pero Tú aumentarás mi fuerza como la del búfalo. Seré ungido con aceite fresco.
Ka ɗaukaka ƙahona kamar na ɓauna; an zubo mai masu kyau a kaina.
11 Y mis ojos mirarán por encima de mis enemigos. Mis oídos escucharán Con respecto a los perversos que se levantan contra mí.
Idanuna sun ga fāɗuwar maƙiyana; kunnuwana sun ji kukan mugayen maƙiyana.
12 El justo florecerá como la palmera. Crecerá como un cedro en el Líbano.
Adalai za su haɓaka kamar itacen dabino, za su yi girma kama al’ul na Lebanon;
13 Plantados en la Casa de Yavé, Florecerán en los patios de nuestro ʼElohim.
da aka daddasa a gidan Ubangiji, za su haɓaka a filayen gidan Allahnmu.
14 Aun en la vejez darán fruto. Estarán llenos de savia y muy verdes
Za su ci gaba da ba da’ya’ya a tsufansu, za su kasance ɗanye kuma kore shar,
15 Para manifestar que Yavé es recto. Mi Roca es. En Él no hay injusticia.
suna shela cewa, “Ubangiji adali ne; shi ne Dutsena, kuma babu mugunta a cikinsa.”

< Salmos 92 >