< Salmos 88 >
1 Oh Yavé, ʼElohim de mi salvación, Día y noche clamo delante de Ti.
Waƙa ce, Zabura ta’ya’yan Kora maza. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat leyannotmaskil na Heman dangin Ezra. Ya Ubangiji, Allah wanda ya cece ni, dare da rana ina kuka a gabanka.
2 Llegue mi oración a tu Presencia. Inclina tu oído a mi clamor.
Bari addu’ata ta zo a gabanka; ka kasa kunne ga kukata.
3 Porque mi alma está harta de aflicciones, Y mi vida se acerca al Seol. (Sheol )
Gama raina yana cike da wahala rayuwata tana gab da kabari. (Sheol )
4 Soy contado entre los que descienden al sepulcro. Soy como un varón sin fuerza,
An lissafta ni cikin waɗanda suka gangara zuwa cikin rami; ni kamar mutumin da ba shi da ƙarfi ne.
5 Olvidado entre los muertos, Como los asesinados que están tendidos en la tumba, De quienes ya no te acuerdas, y son cortados de tu mano.
An ware ni tare da matattu, kamar waɗanda aka kashe da suke kwance a kabari, waɗanda ba ka ƙara tunawa, waɗanda aka yanke daga taimakonka.
6 Me colocaste en la fosa más profunda, En lugares oscuros, en las profundidades.
Ka sa ni a ramin da yake can ƙasa cikin zurfafa mafi duhu.
7 Tu ira pesa sobre mí. Me afliges con todas tus olas. (Selah)
Hasalarka tana da nauyi a kaina; ka turmushe ni da dukan raƙumanka. (Sela)
8 Alejaste a mis conocidos de mí. Me pusiste como un objeto de repugnancia para ellos. Estoy encerrado y no puedo salir.
Ka ɗauke abokaina na kurkusa daga gare ni ka sa na zama abin ƙyama a gare su. An kange ni, ba yadda zan kuɓuta
9 Mis ojos se enfermaron por causa de la aflicción. Cada día te invoco, oh Yavé. Extiendo mis manos hacia Ti:
idanuna ba sa gani sosai saboda baƙin ciki. Ina kira gare ka, ya Ubangiji, kowace rana; na tā da hannuwana zuwa gare ka.
10 ¿Harás milagros a favor de los muertos? ¿Se levantarán los muertos para alabarte? (Selah)
Kakan nuna wa matattu ayyukanka na banmamaki ne? Waɗanda suka mutu sukan tashi su yabe ka ne? (Sela)
11 ¿Se anunciará en el sepulcro tu misericordia, Tu fidelidad en el Abadón?
Ana furta ƙaunar a cikin kabari ne, ana zancen amincinka a cikin Hallaka ne?
12 ¿Serán reconocidas tus maravillas en la oscuridad, Y tu justicia en la tierra del olvido?
An san ayyukanka masu banmamaki a wurin duhu ne, ko ayyukan adalcinka a lahira?
13 Pero yo te invoco, oh Yavé, Clamo por ayuda. De mañana mi súplica llega delante de Ti.
Amma ina kuka gare ka neman taimako, ya Ubangiji; da safe addu’ata kan zo gabanka.
14 ¿Por qué, oh Yavé, desechas mi alma? ¿Por qué escondes de mí tu rostro?
Don me, ya Ubangiji, ka ƙi ni ka kuma ɓoye fuskarka daga gare ni?
15 Desde mi juventud estuve afligido y necesitado. Sufrí tus terrores. Estuve turbado.
Tun ina ƙarami na sha wahala na kuma yi kusa in mutu; na sha wahalar razanarka kuma na kuma fid da zuciya.
16 Tu ardiente ira pasó sobre mí. Tus terrores me destruyeron.
Hasalarka ta sha kaina; razanarka ta hallaka ni.
17 Me rodean de continuo como aguas. En conjunto me cercaron.
Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa; sun mamaye ni ɗungum.
18 Alejaste de mí a mis amigos y compañeros. Solo la oscuridad es mi compañera.
Ka ɗauke abokaina da ƙaunatattuna daga gare ni; duhu ne abokina na kurkusa.