< Salmos 63 >

1 Oh ʼElohim, Tú eres mi ʼEL. Ansiosamente te busqué. Mi alma tiene sed de Ti. Mi cuerpo te anhela en tierra árida y deshabitada, Donde no hay agua.
Zabura ta Dawuda. Sa’ad da yake a hamadar Yahuda. Ya Allah, kai ne Allahna, da nacewa na neme ka; raina yana ƙishinka, jikina yana marmarinka, cikin busasshiyar ƙasar da ta zozaye inda babu ruwa.
2 Así te busqué en el Santuario Para ver tu poder y tu gloria.
Na gan ka a wuri mai tsarki na kuma dubi ikonka da ɗaukakarka.
3 Porque tu misericordia es mejor que la vida, Mis labios te alabarán.
Domin ƙaunarka ta fi rai kyau, leɓunana za su ɗaukaka ka.
4 Por tanto te bendeciré en mi vida. En tu Nombre alzaré mis manos.
Zan yabe ka muddin raina, kuma a cikin sunanka zai ɗaga hannuwana.
5 Como con médula y sustancia está saciada mi alma. Mi boca te alaba con labios jubilosos.
Raina zai ƙoshi kamar da abinci mafi kyau; da leɓunan rerawa bakina zai yabe ka.
6 Cuando en mi cama me acuerdo de Ti, Cuando medito en Ti en las vigilias de la noche.
A gadona na tuna da kai; ina tunaninka dukan dare.
7 Porque Tú eres mi Socorro. Bajo la sombra de tus alas canto con gozo.
Domin kai ne mai taimakona, ina rera a cikin inuwar fikafikanka.
8 Mi alma está apegada a Ti. Tu mano derecha me sostiene.
Raina ya manne maka; hannunka na dama yana riƙe da ni.
9 Pero los que buscan mi vida para destruirla Caerán en las profundidades más bajas de la tierra.
Su da suke neman raina za su hallaka; za su gangara zuwa zurfafan duniya.
10 Serán destruidos a filo de espada. Serán presa de los chacales.
Za a bayar da su ga takobi su kuma zama abincin karnukan jeji.
11 Pero el rey se regocija en ʼElohim. Cualquiera que jura por Él será alabado, Porque las bocas de los que dicen mentiras serán tapadas.
Amma sarki zai yi farin ciki ga Allah; dukan waɗanda suke rantse da sunan Allah za su yabe shi, amma za a rufe bakunan maƙaryata.

< Salmos 63 >