< Salmos 61 >
1 Oh ʼElohim, oye mi clamor. Atiende mi súplica.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Ta Dawuda. Ka ji kukata, ya Allah; ka saurari addu’ata.
2 Cuando mi corazón desmaya, Clamo a Ti desde el extremo de la tierra: Llévame a la Roca que es más alta que yo.
Daga iyakar duniya na yi kira gare ka, na yi kira yayinda zuciyata ta karai; ka bishe ni zuwa dutsen da ya fi ni tsayi.
3 Porque Tú fuiste mi Refugio, Torre fuerte contra el enemigo.
Gama kai ne mafakata, hasumiya mai ƙarfi gāba da maƙiyi.
4 Permite que yo viva en tu Tabernáculo para siempre Y que me refugie al amparo de tus alas. (Selah)
Ina marmari in zauna a tentinka har abada in sami mafaka a cikin inuwar fikafikanka. (Sela)
5 Porque Tú, ʼElohim, oíste mis votos. Diste heredad a los que temen tu Nombre.
Gama ka ji alkawarina, ya Allah; ka ba ni gādo na waɗanda suke tsoron sunanka.
6 Prolongarás la vida del rey. Sus años serán como muchas generaciones.
Ka ƙara kwanakin ran sarki, shekarunsa su kasance a zamanai masu yawa.
7 Estará para siempre delante de ʼElohim. Prepara misericordia y verdad para que lo preserven.
Bari yă yi mulki a gaban Allah har abada; ka sa ƙaunarka da amincinka su tsare shi.
8 Así cantaré alabanza a tu Nombre para siempre, A fin de pagar mis votos cada día.
Sa’an nan zan riƙa rera yabo ga sunanka in kuma cika alkawarina kowace rana.