< Salmos 36 >
1 La transgresión del impío habla a su corazón. No hay temor a ʼElohim delante de sus ojos.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Akwai magana a cikin zuciyata game da zunubin mugu. Babu tsoron Allah a idanunsa.
2 Se jacta ante sus propios ojos De que su iniquidad no será descubierta ni aborrecida.
Gama a idanunsa yana ganin kansa wani abu ne wanda ya sha ƙarfi a gane ko ya ƙi zunubinsa.
3 Las palabras de su boca son iniquidad y engaño. Dejó de ser sabio, de hacer el bien.
Kalmomin bakinsa mugaye ne da kuma ruɗu; ya daina zama mai hikima da yin alheri.
4 Trama iniquidad sobre su cama. Se mantiene en camino no bueno. No aborrece lo malo.
Ko a kan gadonsa ma yana shirya mugunta; yakan sa kansa ga aikata zunubi kuma ba ya ƙin abin da ba shi da kyau.
5 Oh Yavé, tu misericordia llega hasta el cielo, Y hasta las nubes tu fidelidad.
Ƙaunarka, ya Ubangiji, kan kai sammai, amincinka har sararin sammai.
6 Tu justicia es como las montañas de ʼEL, Tus juicios, como inmenso abismo. Tú, oh Yavé, preservas al hombre y la bestia.
Adalcinka yana kama da manyan duwatsu, hukuncinka kamar zurfi mai girma. Ya Ubangiji, kana lura da mutum da dabba.
7 ¡Oh ʼElohim, cuán preciosa es tu misericordia! Por eso los hombres se amparan bajo la sombra de tus alas.
Ina misalin ƙaunarka marar ƙarewa! Mutane manya da ƙanana kan sami mafaka cikin inuwar fikafikanka.
8 Son plenamente saciados con la abundancia de tu casa, Les das de beber del torrente de tus delicias.
Suna biki a yalwar gidanka; kakan ba su sha daga rafin farin cikinka.
9 Porque contigo está el manantial de la vida. En tu luz vemos la luz.
Gama a gare ka akwai maɓulɓular rai cikin haskenka mukan ga haske.
10 Extiende tu misericordia a los que te conocen, Y tu justicia a los rectos de corazón.
Ka ci gaba da ƙaunarka ga waɗanda suka san ka, adalcinka ga masu gaskiyar zuciya.
11 No me alcance el pie de la soberbia, Ni me mueva la mano del inicuo.
Kada ka bari ƙafar mai girman kai yă fāɗa mini, ko hannun mugu ya kore ni.
12 Ahí cayeron los que obran iniquidad, Fueron derribados, Y no pueden levantarse.
Dubi yadda masu aikata zunubi suka fāɗi, a zube, ba za su kuwa iya tashi ba!