< Salmos 121 >
1 Levantaré mis ojos a las montañas. ¿De dónde vendrá mi socorro?
Waƙar haurawa. Na tā da idanuna zuwa wajen tuddai, ta ina ne taimakona zai zo?
2 Mi socorro [viene] de Yavé, Quien hizo [el] cielo y [la] tierra.
Taimakona zai zo daga wurin Ubangiji, wanda ya kafa sama da ƙasa.
3 No permitirá que tu pie resbale, Ni se dormirá el que te guarda.
Ba zai bari ƙafarka tă yi santsi ba, shi da yake tsaronka ba zai yi gyangyaɗi ba;
4 Ciertamente, no se adormecerá ni dormirá, El que guarda a Israel.
tabbatacce, shi da yake tsaron Isra’ila ba ya gyangyaɗi ko barci.
5 Yavé es tu Guardador, Yavé es tu Sombra a tu mano derecha.
Ubangiji yana tsaronka, Ubangiji ne inuwa a hannun damanka;
6 El sol no te fatigará de día, Ni la luna de noche.
rana ba za tă buge ka cikin yini ba balle wata da dare.
7 Yavé te protegerá de todo mal. Él guardará tu alma.
Ubangiji zai kiyaye ka daga dukan masifa, zai tsare ranka;
8 Yavé guardará tu salida y tu entrada Desde ahora y para siempre.
Ubangiji zai kiyaye shigarka da fitarka yanzu da har abada kuma.